Daga Muhammad Farouk
Kasashen Afirka sun bukaci karin Dala biliyan 500 daga Hukumar Bada lamuni ta duniya (IMF) da kuma jinkirta karbar bashin da ake bin su domin shawo kan matsalolin da annobar korona ta haifar musu.
An gabatar da wannan bukatar ce lokacin da ministocin
kudade daga nahiyar Afirka suka gudanar da taro a karkashin Hukumar Tattalin
Arzikin Kasashen nahiyar da kuma Hukumar Bada Lamuni ta duniya kamar yadda RFI
Hausa ta labarto.
Hukumar bada lamunin ta ce asusun da kasashen Afirka ke
bukatar ba su wadannan kudade har Dala biliyan 500 an kirkire shi ne a shekarar
1969 domin tallafawa asusun ajiyar kasashen dake cikin Hukumar.
Ya zuwa yanzu an baiwa kasashen Dala biliyan 281 domin tunkarar
matsalolin da suka addabe su.
Shima bankin Duniya ya bukaci kasashen dake cikin
kungiyar G20 da su taimakawa kasashen masu tasowa wajen amfani da kudaden wajen
fuskantar kalubalen da annobar korona ta haifar domin kare lafiyar jama’ar su.
Ya zuwa yanzu kasashen Duniya 73 suka cancanci daga musu
kafa wajen jinkirta karbar bashin da ake abin su saboda matsalar da annobar ta
haifar.
0 Comments