![]() |
Shaikh Abduljabbar Nasiru Kabara |
Daga
Muhammad Farouk
An yaba wa gwamnatin
jihar Kano da ta dauki matakin shirya mukabala a tsakanin Shaikh Abduljabbar
Nasiru Kabara da hadakar wasu Malamai a jihar dake zarginsa da cin zarafin
Annabi da Sahabbai.
Wata kungiya mai suna
Citizens For Peace and Progress (CIPEP), ta bayyana farin cikinta a cikin wata
takardar sanarwa da jami’inta na yada labarai, Abdullahi Alhassan ya sanya wa
hannu, tana maraba da yadda aka yi amfani da tunani da kuma bin doka da oda ya
dawo a jihar Kano.
A wani sashe na
takardar sanarwar tana cewa; “Biyo bayan tashin-tashinar da aka samu a jihar
Kano saboda haramta wa Shaikh Abduljabbar Nasiru Kabara yin wa’azi a jihar da
gwamnati ta yi da kuma sauyin tunani ya zuwa shirya tattaunawa, mu ‘yan
kungiyar Citizens For Peace and Progress (CIPEP) na sanar da amincewarmu da
matakin komawa ga amfani da tunani da kuma bin doka da oda da gwamnatin jihar
ta yi”, inji sanarwar.
Ya kara da cewa; “jamar’ar
jihar Kano za su shaida cewa Malamin da ake tsangwama na gudanar da harkokinsa,
tare da kula da zaman lafiya wanda wasu Malamai ba su aminta da irin tasa
fahimtar ba game da Hadidai, inda suka zarge shi da cin zarafin Annabi (S) da
Sahabbansa”.
Ya ci gaba da cewa; “Gwamnatin
jihar Kano ta kasance ba ta da zabi da ya wuce ta dirar wa Shaikh Abduljabbar
bayan hadakar Malamai sun zuga ta don gudun ka da Malaman su tunzura jama’a
zuwa ga tashin hankali a jihar in gwamnati ba ta ba su goyon baya ba. Haka
kuma, jama’ar jihar Kano shaidu ne cewa Malamin da ake tsangwama, bisa tabbacin
da yake da shi a kan fahimtarsa game da Hadisan Annabi (S), ya sha kira ga
Malaman su zo a yi mukabala domin tabbatar da gaskiya a tsakaninsu”, inji
kungiyar.
Sai dai kungiyar kuma
ta yi kira ga gwamnatin jihar Kano da ta tabbatar an gudanar da mukabalar bisa
wasu shawarwari da ta bayar domin gujewa tashin hankali da warware matsalar.
Ta ce; “duk Malaman da
suka yi hadaka wurin tsangwamar Shaikh Abduljabbar akan fahimtarsa dole su
halarta. Domin al’umma su tabbatar da adalcin gwamnati da rashin nuna goyon
bayan wani bangare a wannan mataki da ta dauka. Duk Malaman da abin ya shafa
dole su zo da kan su ka da kowa ya turo wani wakili”.
“yada zaman ga al’umma
ta hanyan amfani da rediyo da gwamnati ta ambata za ta yi, ya dace kwarai, kuma
kada ta fasa. Wannan mukabala ya kamata ta jawo bangarorin biyu zuwa ga
fahimtar juna da kuma girmamawa, ba wai za a yi ta ne domin samun wanda ya yi
nasara, ko wanda aka kayar ba. Ya kamata ya zama za a yi ta ne domin al’umma su
ji bambance-bambancen da ke tsakanin fahimtar Malamai, sai su yi wa kansu
hukunci. Idan kuma hadakar Malaman da ke neman a hana Shaikh Abduljabbar wa’azi
suka ki yarda su halarci wannan mukabala, dole kuma gwamnati ta kyale shi ya ci
gaba da harkokinsa yadda ya saba ba tare da wata tsangwama daga gare su ba,”
kamar yadda kungiyar ta fada a takardar
sanarwar.
Daga karshe kungiyar ta
yi kira ga gwamnatin jihar Kano da ta tabbata ta bi wadannan shawarwari domin
kare mutuncinta a idon al’umma da gujewa zargin ta da goyon bayan wani bangare.
Ta ce ta hanyar haka ne kawai za ta iya nuna gaskiya da adalci.
0 Comments