Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Dalilan Da Ya Sanya Muka Ginawa Musulmi Masallaci, Inji Kungiyar CAN

  Yayin da ake samu tsamin dangantaka tsakanin Musulmi da Kirstoci a wasu sassan Nijeriya, shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya ya gi...

 


Yayin da ake samu tsamin dangantaka tsakanin Musulmi da Kirstoci a wasu sassan Nijeriya, shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya ya gina masallaci domin bai wa al’ummar Musulmi damar yin ibada a jihar Adamawa.

Masallacin an gina shi ne a sansanin ‘yan gudun hijira a yankin da ake kira Sangere Margi a garin Girei tare da gina gidaje 86 domin ‘yan gudun hijira da rikicin Boko Haram ya raba su da muhallansu.

Bishop Stephen Dami Mamza shi ne shugaban kungiyar kiristocin Nijeriya reshen jihar Adamawa, ya kuma bayyana dalilan da ya sanya suka gina wannan masallaci, inda ya ce; “akwai wadansu ‘yan gudun hijirar da nake kula da su, akwai kirista akwai musulmi, mun gina musu gidaje 86 ga kuma mun gina musu, mun gina makaranta, mun gina coci. Na gani bai dace kawai mu gina coci ma kirista ba, musulmin da suna tsakaninsu ba su da yawa, amma na ce idan za a bar su su gina masallaci da kansu zai dauke su lokaci kuma watakila zai gagare su, to shi ne na ce ai suma ya dace a gina musu wurin da za su samu su yi ibada”, ya tabbatar.

Gambo Jika, shugaban kungiyar musulmi ta jihar Adamawa, ya nuna jindadinsa bisa wannan, wanda ya ce hakan zai kara fahimtar juna tsakanin musulmi da kiristoci a jihar. Inda ya kara da cewa tabbas hakan abin jindadi bane, abin kuma hada zumunci ne.


No comments