Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Fadar Shugaban Kasa Na Boye Gaskiyar Rashin Lafiyar Buhari, Cewar Kungiyar Kiristoci

  Shugaba Muhammadu Buhari Daga Muhammad Farouk Kungiyar kiristoci ta Nijeriya ‘The Pentecostal Fellowship of Nigeria’ ta zargi fadar ...

 

Shugaba Muhammadu Buhari

Daga Muhammad Farouk

Kungiyar kiristoci ta Nijeriya ‘The Pentecostal Fellowship of Nigeria’ ta zargi fadar shugaban kasa da boye gaskiyar bayanai a kan rashin lafiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Shugaban kungiyar ta PFN, Bishop Wale Oke, ya bayyana hakan ne a Legas a yayin da yake ganawa da kafafen watsa labarai. Ya kuma koka a kan yadda Buhari ya zabi ya rika zuwa kasashen waje neman a duba lafiyarsa maimaikon shugaban ya tsaya ya gyara asibitocin cikin Nijeriya.

Oke har wala yau ya nemi gwamnatin tarayya da ta rika bayyana gaskiya akan rashin lafiyar Buhari saboda a cewarsa hakan ne zai sanya a matsayinsu na kiristoci su san yadda za su yi shugaba Buhari addu’ar samun lafiya.

 “muna yiwa shugaban kasa addu’ar samun koshin lafiya; ya bar kasarnan na fiye da mako biyu kan neman lafiya. Abubuwa biyu ya sanya muka damu da halin da shugaban kasa ke ciki. Mun yadda cewa ba a fadawa kasarnan gaskiya kan rashin lafiyarsa. Muna neman gwamnatin tarayya da fadar shugaban kasa da su baza faifai a kasa su gaya mana me ke damun shugaban kasa. Yanzu shi mutum ne na kowa, akwai bukatar mu san yadda zamu yi masa addu’a. A daina boye mana batun rashin lafiyar shugaban kasarmu, a gaya wa kasar halin da yake ciki domin mu san yadda zamu yi masa addu’a”, inji shugaban kungiyar kiristoci ta PFN.

Kungiyar ta nuna damuwa sosai na yadda ake kai shugaba Buhari kasashen waje domin a duba  lafiyarsa, wanda suka ce hakan babbar barazana ce; “wannan yana nufin shugaban kasarmu ya fi samun aminci a hannun Turawa fiye da hannunmu? Idan wadannan mutane suka yi masa wani abu, me zamu yi ke nan”, suka tambaya.

A karshe ya koka yadda sauran shugabannin Nijeriya suma suke garzayawa kasashen waje da zarar sun ji yanayin rashin lafiya, inda ya ce a maimaikon su rika yin hakan, akwai bukatar su sanya kudin a bangaren lafiya domin bunkasa bangaren.

 

No comments