Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Gwamnati Ta Fara Biyan Mutum Dubu 774 Naira Dubu 20 Duk Wata, Inji Keyamo

  Gwamnatin tarayya ta fara biyan wadanda ta dauka aiki na musamman a shirinta na ‘ Special public works (SPW)’. Festus Keyamo,...

 


Gwamnatin tarayya ta fara biyan wadanda ta dauka aiki na musamman a shirinta naSpecial public works (SPW)’.

Festus Keyamo, karamin ministan kwadago ne ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter a ranar Asabar.

Shirin na SPW shiri ne da gwamnatin tarayya ta bullo da shi kuma ya fara aiki a watan Yulin 2020 inda ta dauki ma’aikata dubu dari bakwai da saba’in da hudu aiki (774, 000) domin gudanar da wani aikin zango a fadin Nijeriya.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da a fara biyan kudaden a wani mataki na rage radadin asarar da cutar korona ta haifar.

A cikin watan Maris din 2021 ne, Keyamo ya ce shugaba Buhari ya bada izinin a fitar da kudaden domin fara biyan wadanda suka amfana da shirin.

Ya ce bayan sakar wadansu ba’adin kudaden ne ga ma’aikatar kudi domin biyan wadanda suka amfana da shirin SPW din, minista Keyamo ya ce sai ya bayar da umurnin fara binciken asusun wadanda za su amfana da kudaden kafin fara biyansu.

 “mun gano wadansu asusun ba su hada shi da lambar sirri na asusun su ba (BVN), wasu kuma sunayen na su ba iri daya bane da lambar BVN dinsu, wasu kuma ba su da BVN”, inji shi.

Ministan ya ce a wani mataki na kawar da rashawa a harkar, ya bukaci Cibiyar horas da ayyuka ta kasa, NDE da su rubuta wasika zuwa ga bankuna domin a gudanar da bincike kafin fara biyan kudaden.

“ya zuwa yanzu Bankin ACCESS ne kawai suka tabbatar da ingancin asusun, inda a yau (Asabar) NDE suka fara biyan kudaden ga wadanda suke da asusu da Bankin ACCESS”, ya tabbatar.

Ya ce sauran bankunan da ya hada da ZENITH, UBA, FCMB, FIDELITY, HERITAGE da Yobe Micro-Finance Banks ana kan bincike.

 


No comments