Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Karya Alkawarin Da Jonathan Ya Yi Ne Ya Sanya Muka Bijera Masa -Babangida Aliyu

Tsohon Gwamnan Jihar Neja, Babangida Aliyu ya bayyana dalilin da ya sa Gwamnonin Jam’iyyar PDP suka bijirewa tsohon shugaban kasa Goo...


Tsohon Gwamnan Jihar Neja, Babangida Aliyu ya bayyana dalilin da ya sa Gwamnonin Jam’iyyar PDP suka bijirewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a shekarar 2015 lokacin da ya tsaya takarar neman wa’adi na biyu.

A wata sanarwar da ya rabawa manema labarai, tsohon Gwamnan ya ce sun dauki matakin ne saboda karyar alkawarin da ya yi cewar ba zai tsaya takara ba bayan kamala wa’adin tsohon mai gidansa Umaru Yar’adua da kuma samun nasarar zaben shekarar 2011.

Babangida ya ce daukacin gwamnonin sun marawa Jonathan baya lokacin da ‘Yar Adua ya rasu da kuma takararsa ta shekarar 2011, amma hakikancewarsa cewar zai zarce a shekarar 2015 ya gamu da fushin su domin hakan ya saba ka’ida kuma hakkinsa ne a matsayin shugaban gwamnonin arewacin kasar ya fito ya yi bayani akai kamar yadda rahoton RFI Hausa ya labarto.

Tsohon Gwamnan ya ce ba wai sun nunawa Jonathan kiyayya bane, sai dai sun dauki matakin ne domin kare muradun jama’ar yankin dangane da alkawarin da suka yi a rubuce wanda aka sanya hannu akai cewar tsohon shugaban ba zai sake takara ba.

Babangida Aliyu ya ce abin takaici ne da yau za a kira sunansa ana cewa shi ne yake adawa da takarar Goodluck Jonathan a shekarar 2015.

Yanzu haka dai Jam’iyyar PDP a karamar hukumar Chanchaga ta dakatar da tsohon Gwamnan saboda abin da ta kira zagon kasa da kuma wasu harkoki da suka sabawa Jam’iyar ta su.

 

No comments