Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Pantami Na Jawo Wa Jam’iyyarmu Ta APC Bakin Jini, A Kore Shi –Jigo A Jam’iyyar

  Wani jigo a jam’iyya mai mulki ta APC, Cletus Obun ya ce ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Isa Ali Pantami na janyo wa ja...

 


Wani jigo a jam’iyya mai mulki ta APC, Cletus Obun ya ce ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Isa Ali Pantami na janyo wa jam’iyyarsu ta APC bakin jini.

Mr Obun, ya bayyana hakan ne a hirarsa da gidan Talabijin na AIT da safiyar ranar Litinin, inda ya ce akwai bukatar a cire Isa Pantami daga mukaminsa ko kuma ya sauka da kansa sakamakon abin da ake zarginsa da shi na goyon bayan ta’addanci.

“Pantami ya sauka daga mukaminsa, idan kuma ya ki sauka, a cire shi! Ka da a yarda ya ci gaba da bata sunan gwamnatin nan”, inji shi kamar yadda MADOGARA ta labarto.

Mr Obon ya ce idan za a iya tunawa, sauka daga mukaminta da tsohuwar ministar kudi ta yi, Kemi Adeosun ya biyo bayan zarginta da aka yi cewa ba ta hidimtawa kasa ba (NYSC).

Kiran na Mr Obun ya biyo bayan kiran da jam’iyyar PDP ta yi inda ta bukaci da a kori Pantami daga mukaminsa.

Shi da Isa Ali Pantami na fuskantar wadannan kiraye-kiraye na a cire shi daga mukaminsa ne tun bayan da wadansu kafafen watsa labarai suka wallafa wadansu bidiyoyinsa da ya yi a shekarun da suka gabata, inda yake goyon bayan wadansu  kungiyoyin ta’addanci na AlQaeda da kuma Taliban.

Biyo bayan bayyanar bidiyon, Isa Ali Pantami ya bayyana cewa ya yi nadamar wadannan fatawowi da ya yi sakamakon lokacin da ya yi su yana da ‘karancin shekaru’, kuma yana da karancin fahimtar wadansu abubuwan da suka gudana.

 Karanta labarin nan; Na Yi Nadamar Kalaman Da Na Yi Kan Goyon Bayan AlQa'eda Da Taliban A Baya -Pantami

No comments