Tsohon
Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta
dawo da tsoffin hafsoshin soji a matsayin mafita ga kalubalen tsaro da kasar ke
fuskanta.
Atiku
Abubakar, wanda shi ma tsohon dan takarar shugaban kasa ne, ya yi wannan kiran
ne a cikin wata sanarwa a kan "tabarbarewar yanayin tsaro" a ranar
Talata kamar yadda RFI Hausa ta labarto.
Atiku
Abubakar yace “yanayin tsaro a Nijeriya yana tabarbarewa cikin sauri kuma
talakawan Najeriya suna rayuwa cikin fargaba game da rayukansu da na‘ yan
uwansu. Babu inda ake da kwanciyar hankali, kama daga Gonaki da kasuwanni da
makarantu cikin gidaje da masallatai, majami'u, da kuma birane duk abin ya
shafa.
Atiku
Abukar ya kara da cewa: “Yan ta’adda na ci gaba da fafada yankunansu sama da
Arewa maso gabas, zuwa yankuna masu nisa har zuwa jihar Neja a Arewa ta
tsakiya, mai nisan ‘yan tafiyar sa’o’i daga Babban Birnin Tarayya"
Tsohon
mataimakin shugaban kasar yace, "Yanzu lokaci ya yi da za a yanke hukunci
game da shugabanci, inda ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta yi la’akari da
tuna daukacin tsoffin sojoji maza da mata, wadanda ke da niyyar komawa bakin
aiki, domin taimakawa dakarun dake fafatawa da ayyukan tsageru ta kowane
kusurwa, har sai sun samu nasara.
Nijeriya
Nada Gwarazan Tsoffin Sojoji
Ya
ce, a matsayinsa na tsohon mataimakin shugaban kwamitin tsaro na kasa,
"yana sane da cewa Najeriya tana da dimbin gwarazan tsoffin sojoji,
wadanda suka samu horo a gida da waje kuma har yanzu suna nan da ransu".
Ya
ce babu wani amfani na barin wannan damar ta sukurkuce, alhali kasa na cikin
wani yanayi.
0 Comments