Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Auren Sirri Da Sani Danja Ya Yi Shi Ya Raba Aurensa Da Mansurah Isah

Wasu Majiyar Zuma Times Hausa da ta hada da Mujallar Fim sun bayyana cewa tsofafin jarumai na Kannywood, Sani Danja da Mansura Isa sun d...


Wasu Majiyar Zuma Times Hausa da ta hada da Mujallar Fim sun bayyana cewa tsofafin jarumai na Kannywood, Sani Danja da Mansura Isa sun dade da rabuwa inda Mansura ta koma gidan haya da zama tare da 'ya'yanta hudu.

An ce dalilin rabuwarsu na da alaka da auren sirri da Sani Danja ya yi a Kaduna ba tare da sanin Mansura ba har sai da matar ta haihu.

Majiyar ta ci gaba da cewa Mansura ta yi alkawari ba za ta ba shi ko daya daga cikin ‘ya’yan ba.

Wadanda ke kusa da Mansura sun bayana cewa ba wannan ne farko da Sani Danja da Mansura suka rabu ba don ko a baya ya taba sakinta.

Zuma Times Hausa ta samu karin bayani da ke cewa Mansura ta gaji da halayen mijinta ne don yadda ya sake mata hidimomin gida inda ta ke daukar dawainiyyar tafiyar da al'amuran gidan.

Bincike ya nuna cewa Mansura dai mace ce mai kokarin neman na kanta da taimakawa marasa karfi.

Duk kokarin da majiyar ta yi ta don jin na bakin ma'auratan ya ci tura.

1 comment

  1. Ubangiji Allah Ya kyauta, Allah Ya qara la'antar shedan la'ananne wanda bai qaunar sunnar Manzon Allah (SAW).

    ReplyDelete