Shugaban
kasa Muhammadu Buhari ya amince da a kafa hukumar takaita yaduwar kananan
makamai a kasar.
A sanarwar
da mai taimaka wa shugaban kasar kan shafukan sada zumunta, Bashir Ahmad, ya
wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Litinin, ya ambato Kakakin ofishin mai bai
wa shugaba Buhari shawara a kan sha'anin tsaro yana cewa hukumar za ta kasance
a karkashin ofishin na su.
Hukumar
za ta maye gurbin kwamitin shugaban kasa kan dakile yaduwar kananan makamai, in
ji sanarwar.
Kafa
hukumar "na cikin matakan inganta tsaron Nijeriya domin magance barazanar
tsaro da kuma karfafa shirin da kasashen yankin ke yi wajen takaitawa da magance
matsalar yaduwar kananan makamai," a cewar sanarwar.
A baya
dai Shugaba Buhari ya sha kokawa kan karakainar kananan makamai da ma manya
cikin kasar, lamarin da ya ta'allaka da yakin da aka yi a kasar Libya.
Hukumomi
sun bayyana cewa akwai dubban kananan makamai a hannun 'yan kasar, abin da ke
ta'azzara hare-hare da kuma yin barazana ga zaman lafiyar Nijeriya, BBC ta labarto.
0 Comments