Daga Auwal Adam
Kamar yadda suka saba a duk shekara,
mabiya Harkar Musulunci a Nijeriya da aka fi sani da ‘yan shi’a almajiran
Shaikh Ibraheem Zakzaky sun gudanar da muzaharorin nuna goyon baya ga al’ummar
Falasdinu kan mamayar da haramtacciyar gwamnatin Isra’ila ke yi musu.
Jerin gwanon na su wanda suka saba
yi a duk Juma’ar karshen watan Ramadan, a bana ma sun gudanar da shi a garuruwa
da dama da ya hada Kano, Kaduna, Abuja, Zariya, Jigawa, Katsina, Sakkwato,
Bauchi, Jos, Nasarawa, da sauran su.
A yayin jerin gwanon na su sun rika
wakokin nuna goyon baya ga Falasdinu da la’anta ga Amurka da kuma Isra’ila.
Wakilanmu sun labarto mana cewa; a karshen rufe wannan muzaharar an kona
tutocin Amurka da Isra’ila a wani mataki na Allah-wadai da abin da Isra’ila ke
yi bisa goyon bayan Amurka.
Har wala yau masu muzaharar sun rika
raba takarda kan dalilin fitowar na su. Takardar mai taken; ‘YANCI GA KUDUS,
’YANCI GA SHAIKH ZAKZAKY!’, Shaikh Abdulhamid Bello ne ya sanya mata hannu.
Ga cikakken
bayanin da takardar ta kumsa kamar yadda suka raba;
‘YANCI GA KUDUS, ’YANCI GA SHAIKH
ZAKZAKY!’
A wannan wata na Ramadan, al’ummar
musulmi masu kishi sukan shirya tarurrukan gangami da muzaharori na lumana don
fadakar da jama’a irin mamayar da Yahudawan Sahayoniya suke yi wa masallacin
Kudus mai tsarki. A shekarar 1979, Imam Khomeini ya ayyana ware kowace Juma’ar
karshe ta watan Ramadan a matsayin Ranar Kudus, kuma ya yi kira ga Musulmi a
duk fadin duniya da su rika yin gangami kan haka. Tun sannan kuma Jagoran Harka
Islamiyya, wanda ake tsare da shi a yanzu, Shaikh Ibraheem Zakzaky, ya rika
shirya gangami da muzaharori na Ranar Kudus kawo yanzu. To, a yau Ranar Kudus
ta zama wata rana da duniya ke hakkakawa. Wannan gangami ya zama wani bangare
na gwagwarmayar Musulmi masu kishi don ganin gaskiya da adalci sun tabbata a
duniyar da zalunci da rashin bin doka suka mamaye.
Don haka muna kira ga al’ummar
musulmi da sauran jama’a masu kaunar gaskiya da adalci a duk fadin duniya su
shigo wannan tafiya a yi da su. To, me ya sa? Saboda Kudus ko Jerusalem, tamkar
zuciya ce ta Musulunci da al’ummar musulmi. Matsayinta a kowane zamani yana
nuna irin kyautatuwar halin da al’ummar Musulmi suke ciki. Su kuwa makiya sukan
hari ita wannan zuciya ce a duk lokacin da yanayi ya ba da damar hakan a tsawon
tarihi. Ma’ana irin halin mamaya da danniya da Kudus ke ciki a yanzu, shi ne
halin da al’ummar Musulmi a kusan duk fadin duniya suke ciki.
Dalili na biyu kuma shi ne, kalmomi
ba za su iya cikakken bayanin irin mummunan halin da Palasdinawa suke ciki a
Palasdinu da ke karkashin mamayar Yahudawan Sahayoniya. A ‘yan kwanakin nan ma
sai da kungiyar kare hakkin dan Adam mai suna HRW a takaice, ta fitar da wani
rahoton shekara-shekara, inda ta kara tabbatar da abin da muka dade muna fada a
irin wannan gangamin, cewa Jami’an gwamnatin Isra’ila suna aikata laifukan yaki
na nuna wariyar addini da danniya, wadanda dukkanin biyun nan laifukan yaki ne
ga dan Adam.
A tsawon fiye da gomomin shekaru
akwai fassarar kasa da kasa da ta bayyana nuna wariya a matsayin wani laifi
idan Jami’an wata hukuma bisa tsari suna danne wata jama’a a wani yanki da suke
da iko a kai, kuma suna cin zarafin su da nufin tabbatar da iko a kan jama’ar
da ake dannewar don amfanin jama’ar da ke yin danniyar. Don kawo sauyi na
gaske, dole mu bayyana lamarin a hakikanin yadda yake: Tsarin Isra’ila wani
tsari ne na danniya da nuna wariya wanda kuma bai nuna alamun gushewa ba, wanda
kuma a hakikanin gaskiya ya shiga cikin fassarar nuna wariya na addini.
Alal hakika kasashen duniya a tsawon
shekaru sun yi ta shashantar da duk wani rahoton danniya daga Palasdinu tare da
kau da kai daga lamarin, wanda ake ganin sa a kusan kullum. A halin yanzu fa a
kowace rana a yankin Gaza na Palasdinu akan haifi yaro ne tamkar a kurkuku mara
rufin sama, in kuma a yankin Yammacin kogin Jordan ne, to ba shi da wasu
hakkoki na kowane dan kasa, in kuma a Isra’ila ne, to ana haihuwar sa a
matsayin mara daraja a idon doka, in kuma a kasashen da ke ketare ne, to ana
haihuwar sa a matsayin dan gudun hijira ne, tamkar iyayensa da kakanninsa,
saboda kawai shi Bapalasdine ne ba Bayahude ba.
Lalle kam Harkar Musulunci ta duniya
na da sauran jan aiki a gabanta kafin ta kai ga ganin nasarar gwagwarmayar da
take yi na ’yanta Palasdinu daga danniya da mamayar Yahudawan Sahayoniya. Amma
kafin nan dole sai an samu kasashen Musulmi da dama da suka samu gagarumin
sauyi shigen irin wanda Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta samu. Duk ran da aka ce
duniyar Musulunci ta dawo da lafiyarta, dole kanwar na ki za ta sa Yahudawan
Sahayoniya su nemi sulhun zaman lafiya, kasashen Yammacin Turai su turo jiragen
ruwa da na sama don kwashe su daga yankin Palasdinu, ita kuma Amurka ta yi musu
tayin ware musu yankunan kasarta inda za su zauna.
A karshe, a yayin da muke wannan
muzahara ko gangami, muna kara jaddada kiran da muka shafe shekaru biyar
mawuyata muna yi na a saki Jagoranmu, Shaikh Ibraheem Zakzaky, matarsa da
sauran ‘yan’uwa maza da mata da ake tsare da su tun bayan kisan kiyashin Zariya
da gwamnatin Buharin nan ta aiwatar a Disamban 2015. Shaikh Zakzaky bai aikata
laifin komai ba, kamar yadda wata babbar kotun Abuja ta tabbatar tun 2016, don
haka a bar shi ya tafi gida a matsayin Malami mai cikakken ’yanci.
SA HANNU
SHAIKH ABDULHAMID BELLO ZARIA
07/05/2021
0 Comments