Isra’ila Na Ci Gaba Da Zaluntar Falasdinawa A Harabar Masallacin Kudus

 


Kungiyar Hamas ta Falasdinawa ta gargadi ga Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu akan cewa kada ya yi wasa da wuta bayan da Yahudawan Isra’ila suka raunata Falasdinawa kusan 200 a harin da Ć´an sandan Isra'ila suka kai musu a Kudus a ranar Juma'a.

Shugaban Hamas, Ismail Haniyeh ya ce, Falasdinawa za su ci gaba da ba da kariya ga unguwar Shaikh Jarrah da ke gabashin Kudus da aka mamaye, inda Isra’ilawa Ć´an kama wuri zauna ke ikirarin filayensu.

Isra’ila na ci gaba da zaluntar Falasdinawa din kan yiwuwar korar Falasdinawa daga yankin. Mafi yawan wadanda Isra’iliyawa suka raunata sun raunata su ne a harabar masallacin al-Aqsa lokacin da Ć´an sanda suka buÉ—e wuta da harsasai.

Post a Comment

0 Comments