Ministan
shari’ar NIjeriya, Abubakar Malami ya ce binciken da suka gudanar ya nuna musu
wasu fitattun 'yan NIjeriya da kuma 'yan kasuwar da ke daukar nauyin ayyukan
ta’addanci a cikin kasar.
Ministan
ya ce tuni aka fara shirin gurfanar da wadannan mutane a gaban kotu domin
fuskantar shari’a akan rawar da su ke takawa wajen haifar da tashin hankali
sakamakon binciken da gwamnati ta gudanar a Daular Larabawa dangane da masu
daukar nauyin bai wa boko haram kudade.
Wannan
matsayi na gwamnati na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fuskantar karuwar
hare-haren ayyukan ta’addanci na Boko haram a yankin arewa maso gabas da kuma
wasu hare-haren na daban a wasu yankuna musamman arewa maso yamma.
Malami
ya ce gwamnati ta dauki dogon lokaci ta na gudanar da bincike akan wannan
lamarin da ya shafi ayyukan ta’addanci bayan da kotu a Daular Larabawa ta daure
wasu 'yan Nijeriyar guda shida.
Ministan
ya ce binciken da suka dauki dogon lokaci su na yi ya nuna musu wasu mutane da
hukumomi da ke da hannu wajen jefa kasar cikin tashin hankali.
Malami
ya ce suna da kwararan shaidu da ke nuna musu irin wadannan mutanen da ke
daukar nauyin baiwa 'yan ta’adda kudade kuma yanzu kotu ce za ta tabbatar da
wannan zargi.
0 Comments