Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Na Yi Nadamar Dawowa Nijeriya Na Karbi Mukamin Siyasa –Pantami

  Daga Muhammad Farouk Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Isa Ali Pantami ya bayyana nadamarsa bisa karbar mukamin siyasa da y...

 


Daga Muhammad Farouk

Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Isa Ali Pantami ya bayyana nadamarsa bisa karbar mukamin siyasa da ya yi a Nijeriya.

Minista Pantami ya bayyana hakan ne a wani sakon Bidiyo da MADOGARA ta samu wanda aka wallafa a shafin YouTube, inda ministan ya nuna damuwarsa bisa wannan hukunci da ya yanke na dawowa Nijeriya daga Madina domin ya yi wa kasarsa hidima.

Pantami ya ce; “mafi tsaurin mataki da na dauka a duk duniya a rayuwata zuwa yau shi ne na dawo Nijeriya daga garin Madina saboda ana bukatar gudummawata a gida. Ban taba daukar wani mataki a rayuwata da ya ba ni wahala irin wannan ba. Saboda duk yawon da na yi a duniya, na shiga kasashe birjik, ban taba shiga garin da nake son sa ba, Allah ya jarabce ni nake son na rayu a cikinsa irin garin Madina ba”, ya tabbatar.

Minista Isa Ali Pantami ya ci gaba da cewa; “watarana salloli guda biyar gaba daya a masallacin Manzon Allah nake yin su. Dukkaninsu guda biyar. ‘Ya’yana masu wayo a masallacin Annabi (SAW) suke haddar Alkur’ani. Yara a nan suke, iyalanka a nan suke zuwa su yi sallah. Duk kwana hudu, biyar zuwa shida a karshen mako sai ka je Makkah ka yi Umarah. Watarana sai karfe daya na dare za ka kama hanya saboda amincin wurin”, ya tabbatar.

Minista Pantami bai tsaya nan ba, ya ci gaba da cewa; “kuma abin da ake ba ka na yau da kullum a matsayin albashi da alawus, wallahil azim ba na iya kashe kashi 25 a cikin 100. Duk yadda nake jin dadi a wurin, na je Makkah, na sauka a duk sati a Darur Tauhid ko zamzam ne ko kuma Hilton, bana kashe kashi 25 na abin da ake ba ni. Wahalar sha’ani shi ne ba inda ya kai gida. Idan kowa ya guji gida, to wa zai zo ya bayar da gudummawa wajen rage matsalar gidan?” ya tambaya.

Ya ci gaba da cewa; “kuma duk kasar da ka gani a duniya ‘yan kasar ne suka yi hakuri suka tsaya suka gyarata. Amma ba a taba gyara wani gari a duniya kowanne dan gari ya ce shi zai bar garin ya koma wani wuri ya zauna ba. Ba a taba gyara da haka ba”, ya jaddada.

Minista Pantami har wala yau a wani bangare na bayaninsa, ya kara da cewa; “dole ne sai an hakura da wadansu abubuwa. An hakura amma har yanzu ina jin radadin a zuciyata yana damuna! Har yanzu! Wani lokaci a yanzu haka ko a TV (talabijin) aka nuno Madina, ana sallah, wallahil azim sai na ji kwalla”, ya lurantar.

Ya kara da cewa; “Rashin hakuri idan na zauna, da muna da irin ‘group’ na abokan aikinmu da muke zuwa masallaci mu yi sallah tare, akwai wadansu ‘yan Ingila irin su Abdullahil Na’amun, Dakta ne, su Dr Muhammad Buna’id, su Dr Ali Tufayl, aminaina ne, kullum zamu fito daga ofis sai a shiga mota a je harami minti biyar an isa masallaci an yi sallah an dawo. Kawai da karatu zamu fito mu shiga sallah. Idan na ga sun yi ‘posting’ a ‘group’ sun ce ku sauko mu shiga masallaci, kawai sai ya zama duk abin da nake sai na gagara, saboda me? Saboda ina tuna wadannan ‘moment’ din, haka na yi ta zare kaina a ‘group’ din ba zan iya zama ba. Saboda me? Abin da ya fi min radadi shi ne wannan!”

Har wala yau Pantami ya nuna yadda a kowanne yini mafi kankantar sallar da suke samu shi ne sau hudu kowanne wuni, ya ce wani lokacin duka khamsul salawat a masallacin Annabi zaka yi su; “akwai ribar da ya kai wannan?” ya tambaya.

“gidan da nake zaune zuwa rijiyar Sayyidina Usman, wanda ya siya Annabi ya ce makomarsa aljanna ne, ba na kai minti biyu ko uku nake isa wurin. Ina zaune a Faisaliya, anguwar da nake ga ni ga Jami’a, hanya ce tsakani da Jami’a, idan na koma daya bangaren, kusa da Jami’a gidan gwamnan Madina ne. Idan ban je harami ba, a nan tare da shi muke sallah. To ka fito a wannan hali din, ka bar damar ka zo, Allah dai yasa mu dace. Allah ya karbi wannan a matsayin ibada. Amma ba abu ne mai sauki ba gare ni har yanzu!” inji Minista Pantami.  

Cikakken bayanin cikin bidiyo; 




2 comments

  1. Jarabawa ce malan Allah yabaka ikon cinye ta

    ReplyDelete
  2. Malam jarabawa ce. Allah ya san za ka iya Shi yasa ya daura .muna maka fatan alkhairi Kuma Allah ya tsareka da ga dukkan makirci Mai makirci

    ReplyDelete