Daga Muhammad Farouk
Gwamnatin
Jihar Kaduna ta ce wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe mutum biyu tare
da raunata wasu maza shida a wasu hare-hare daban-daban da suka kai kananan
hukumomin Chikun da Kajuru ta jihar.
Kwamishinan
Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Samuel Aruwan ne ya tabbatar da faruwar lamarin a
cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Talata a Kaduna.
Mista
Aruwan ya ce jami'an tsaro sun ba da rahoton cewa 'yan bindiga sun mamaye
Mazari, wani gari kusa da Buruku a karamar hukumar Chikun, mutum daya ya mutu a
harin, sannan wasu uku sun jikkata.
Ya
bayyana cewa a wani lamarin, yan fashin sun kai hari a kauyen Doka, karamar
hukumar Kajuru, sun kashe mutum daya tare da raunata wasu uku.
Jihar
Kaduna dai na daya daga cikin jihohin da ke fama da matsalar 'yan bindiga a jihohin
kasarnan. Kuma daruruwan mutane ne 'yan bindigar suka kashe ko suka yi garkuwa
da su a cikin' ‘yan shekarun nan.
Sauran
jihohin da irin wannan ta'addancin ya shafa sun hada da Neja, Zamfara da
Katsina da Sakkwato.
0 Comments