Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Jami’ar Maryam Abacha Ta Yi Jajen Mutuwar Shugaban Kasar Zambia Na Farko, Dr Kenneth Kaunda

  Hukumar gudanar da jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN) ta jajantawa gwamnati da dukkanin al’ummar kasar Zambia bisa rasuwa...

 


Hukumar gudanar da jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN) ta jajantawa gwamnati da dukkanin al’ummar kasar Zambia bisa rasuwar shugaban kasar na farko, Dr Kenneth David Kaunda, wanda ya mutu yana da shekara 97 na duniya.

Kauda ya mutu ne a asibitin sojoji dake Lusaka a ranar Alhamis din 17 ga watan Yuni bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.

Sakon jajen na dauke ne da sa hannun shugaban Jami’ar kuma mu’assasin jami’ar Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo a takardar da ya rabawa manema labarai a Kano a ranar Asabar.

A cewar sanarwar, mutuwar Kauda babban rashi ne ga al’ummar Afrika da kuma kasar ta Zambia duba da yadda suka rasa dan kishin kasa kuma jajirtacce wanda ya bayar da gudummawa da dama wajen ci gaban kasar sa.

"shugaba Kaunda shi ne shugaban kasar Zambia na farko kuma babban jigo ne wajen fafutikar samar da ‘yancin kasar wanda gudummawarsa wajen ci gaban kasar ya fi karfin a misalta”, inji sanarwar.

"Shugaban Jami’ar Maryam Abacha American University na Nijeriya, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo a madadin hukumar gudanar da jami’ar muna mika sakon jajenmu ga iyalan Marigayin, da kuma al’ummar Zambia bisa rashin Dr Kenneth Kauda," sanarwar ta jaddada.

A karshe Farfesa Abubakar Gwarzo ya yi addu’ar ci gaba da samun zaman lafiya, hadin kai da kuma daidaito tare da bunkasar tattali arziki da ci gaba mai amfani ga al’ummar Zambia da ma nahiyar Afrika baki daya.

No comments