Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Rikicin Boko Haram Ya Hana Manoma Fiye Da Dubu 65 Zuwa Gonakinsu, inji FAO

  Hukumar Bunkasa Noma ta Majalisar Dinkin Duniya FAO, ta yi gargadi game da karancin abinci a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya. FAO ta...

 


Hukumar Bunkasa Noma ta Majalisar Dinkin Duniya FAO, ta yi gargadi game da karancin abinci a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

FAO ta ce matsalar Boko Haram ta hana manoma kimanin dubu 65 da 800 samun gudanar da ayyukan gona a yankin.

Wakilin FAO a Nijeriya, Fred Kafeero ne ya bayyana haka yayin bikin kaddamar da ayyukan noman rani na wannan shekara a Maiduguri.

Rahoto kan halin da noma ke ciki a Arewa maso Gabashin Nijeriyar na zuwa ne a daidai lokacin da mazauna karamar Hukumar Kala Balge a Jihar Borno ke kokawa kan yadda Giwaye suka addabi ayyukansu na noma, kamar yadda Kaumi Ali Ngalama ya shaidawa sashin Hausa na RFI.

Yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya dai na daga cikin yankunan da manomansu suka amfana da shirin tallafawa bunkasar ayyukan nom ana Ancho Borrower da aka kaddamar a karkashin jagorancin babban bankin kasar CBN fiye da shekaru 3 da suka gabata.

No comments