Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

‘Rikicin Boko Haram Ya Lakume Rayukan Kananan Yara Dubu 324’

  Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana yadda rikicin shekaru 12 da yankin arewa maso gabashin Nijeriya ya fuskanta ya lakume rayu...

 


Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana yadda rikicin shekaru 12 da yankin arewa maso gabashin Nijeriya ya fuskanta ya lakume rayukan kananan yara dubu dari 3 da 24 galibinsu wadanda shekarunsu ya fara daga biyar zuwa kasa.

Rahoton ya bayyana cewa, alkaluman kari ne kan mutum dubu 40 da hare-haren Boko Haram ya kashe daga shekarar 2009 zuwa yanzu baya ga wasu mutum miliyan 2 da rikicin ya raba da muhallansu.

Rahoton na Majalisar Dinkin Duniya ya ce galibin kananan yaran sun mutu ne sanadiyyar cutukan da ke musu barazana ciki har da kyanda baya ga yunwa da rikicin na Boko Haram ya haddasa tsanantarta a yankin.

Rahoton na Majalisar Dinkin Duniya wanda aka yiwa take da ‘‘Illar da rikici ya haifarwa ci gaban yankin arewa maso gabashin Nijeriya’’, ya ce kashi 90 na wadanda rikicin shekarun 12 ya salwantar da rayukansu kananan yara.

Sashen shirin bunkasa birane na Majalisar da ya jagoranci fitar da rahoton, ya ce rikicin na Boko Haram ya kassara harkokin Noma da cinikayya da kuma samar da abinci wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen haddasa yunwa tsakankanin biranen da suka dogara da yankin.

A cewar sashen akwai sauran illolin da yakin na shekaru 12 ya haifarwa yankin baya ga kisan daruruwan mutanen da kuma wadanda suka rasa matsugunansu.


No comments