Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kachia Ta Jihar Kaduna

  ‘Yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hari kauyen Awon dake Yankin Kachia ta Jihar Kaduna inda suka hallaka mutum guda tare da sa...

 


‘Yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hari kauyen Awon dake Yankin Kachia ta Jihar Kaduna inda suka hallaka mutum guda tare da sace mutum 12.

Sarkin Kachia Idris Suleiman ya ce maharan sun fara kai hari ne wani gidan biredi a kauyen Awon inda suka hallaka mutum guda da kwashe wasu mutane 5, yayin da daga bisani suka kara gaba inda suka kwashe wasu mutane 28 a bakin kasuwa cikin su harda mace guda mai dauke da juna biyu.

Suleiman ya ce bayan kashe mutum guda da kuma kama wasu da suka yi garkuwa da su, ‘yan bindigar sun kuma saci kayan dake shagunan mutane bayan sun gudu domin tsira da rayukan su.

Kakakin ‘yan Sandan Jihar Kaduna Mohammed Jalige ya tabbatar da aukuwar lamarin inda ya ce maharan da suka kai harin na dauke ne da muggan makamai.

A sanarwar da ya rabawa manema labarai Jalige ya ce dakarunsu sun bi bayan ‘yan bindigar inda suka kubutar da mutane 2, yayin da ake ci gaba da farautar su domin kubutar da sauran.

‘Yan bindigar da suka addabi yankin arewa maso yammacin Nijeriya na ci gaba da kai hare-hare a wasu sassan jihar Kaduna inda suke kashe fararen hula da kuma garkuwa da wasu domin karbar kudin fansa.

Daga cikin wuraren da ‘yan bindigar ke kai hari yanzu haka bayan tare hanya suna kwashe fasinjoji harda makarantu inda suke dibar dalibai kamar yadda aka gani a Kwalejin aikin noma da Jami’ar Greenfield a baya bayan nan, bayan na Jihohin Katsina da Neja da kuma Kebbi.

No comments