Daga Ammar Muhammad
Jaridar MADOGARA a rahoton ta na safiyar yau Litinin ta yi hasashen cewa; akwai yiwuwar
a soke hawan babbar sallah a masarautar Zazzau biyo bayan shawarar da kwamitin yaki da cutar korona na
gwamnatin Tarayya a karkashin Ofishin Sakataren Gwamnati, Boss Mustapha ta bayar saboda dawowar cutar a karo na uku samfurin Delta.
Kwamitin
yaki da korona ta bayyan jihohi bakwai dake fuskantar hadarin cutar ciki kuwa
harda jihar Kaduna.
Bayan
bullar rahoton MADOGARA, kwatsam da ranar yau Litinin, Masarautar Zazzau ta bada
sanarwar cewa; Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambassada Ahmad Nuhu Bamalli da
majalisarsa sun yi taro sun tsayar da shawarar cewa; “an soke hawan Babban Sallah na bana da aka
shirya za a gudanar a ranar Talata 10 ga
watan Zulhijjah, 1442 daidai da 20 ga watan Yulin 2021. Saboda
haka ba za a gudanar da hawan sallah ba”, inji sanarwar.
Masarautar
ta bayyana dalilai biyu da suka sanya
aka soke hawan wanda ta ce; “an soke hawa saboda dalilai na rashin tsaro
da kuma matsala da ta taso na al’amarin cutar mai sarke numfashi (COVID-19
Pandemic)”, suka nusasshe.
Sai dai
masarautar ta ce za a gudanar da sallar idi Babba kamar yadda aka saba a
dukkanin masallatan da aka saba a kasar ta Zazzau.
“Mai
Martaba Sarkin Zazzau na umurtan
dukkanin Hakimai masu kasa da su yi sallah Babba a gundumarsu tare da jama’arsu. Ana kira da a ci gaba da kiyaye
dokokin cuta mai sarke numfashi. A kuma ci gaba da yiwa kasa addu’ar zaman
lafiya, da fatan Allah ya kawo mana karshen wadannan fitintinu dake addabar kasar mu, Amin”, inji
takardar.
Alhaji
Barau Musa Aliyu, Sarkin Fulanin Zazzau, kuma Sakatare na masarautar shi ne ya
sanya takardar hannu kuma aka aikawa dukkanin Hakimai dake karkashin
masarautar.
![]() |
Kwafen Takardar |
0 Comments