BBC Hausa ta labarto cewa; Cutar kwalara ta kashe mutum 325 a Najeriya tun daga watan Janairun 2021 zuwa 27 ga watan Yuni, a cewar Dr Chik...
BBC Hausa ta labarto cewa; Cutar kwalara ta kashe mutum 325 a Najeriya
tun daga watan Janairun 2021 zuwa 27 ga watan Yuni, a cewar Dr Chikwe Ihekweazu
shugaban hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta NCDC.
Dr Ihekweazu ya faÉ—a wa kamfanin labarai na NAN ranar Asabar cewa
an samu mutum 1,786 da suka kamu da cutar a jiha shida daga 20 zuwa 26 ga watan
Yuni.
Jihohin su ne: Bauchi (1,239), Kano (362), Neja (62), Zamfara (55),
Kaduna (59), Filato (9).
A cewarsa, daga 13 zuwa 19 ga Yuni, jiha biyar - Bauchi, Kano,
Kaduna, Filato, Zamfara - sun samu mutum 1,757 da ake zargin sun kamu da cutar.
Jihohin da cutar ta ɓulla zuwa yanzu su ne: Benue, Delta, Zamfara,
Gombe, Bayelsa, Kogi, Sokoto, Bauchi, Kano, Kaduna, Filato, Kebbi, Cross-River,
Nasarawa, Neja, da kuma Abuja.
No comments