Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

'Akalla Mutum Dubu 24 Ne Suka Ɓace A Nijeriya Sakamakon Rigingimu'

  BBC Hausa; Ƙungiyar agaji ta kasa da kasa ICRC ta ce sama da mutu dubu 44 yanzu haka sun ɓata a sassan Afirka - sama da kashi 45 cikin 10...

 


BBC Hausa; Ƙungiyar agaji ta kasa da kasa ICRC ta ce sama da mutu dubu 44 yanzu haka sun ɓata a sassan Afirka - sama da kashi 45 cikin 100 na wannan adadi yara ne.

ICRC ta ce kashi 82 cikin 100 na mutanen da ta dau rajistar ɓatawarsu sun fito ne daga ƙasahe bakwai da ke fama da rikicin ƴan bindiga.

A wata sanawar da ta fitar kan ranar tunawa da mutanen da suka bata a duniya a wannan Litinin din, ICRC ta ce sama da rabin wannan adadi na mutane da suka ɓata ƴan Najeriya ne.

Sauran ƙasashen da aka samu ɓatarwa mutanen sun hada da Ethiopia da Sudan ta Kudu da Somalia da Libya da DR Congo da kuma Kamaru.

Hukumar ta ce nahiyar Afirka na ganin karuwar mutanen da ke ɓatawa a shekarun baya-bayanan saboda rashin zaman lafiya da wasu rigingimun.

Sannan yanayin da ake na annobar korona na dakile kokarin binciko su domin sake sadasu da iyalansu.

No comments