Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

An Yi Artabu Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga A Filato

  Dakarun sojin Nijeriya sun kashe 'yan bindiga   shida bayan ‘yan bindigar sun kashe wadansu 'yan sanda uku masu farin kaya, wadand...

 


Dakarun sojin Nijeriya sun kashe 'yan bindiga  shida bayan ‘yan bindigar sun kashe wadansu 'yan sanda uku masu farin kaya, wadanda suka je bincike a yankin karamar hukumar Mangu.

‘Yan ta’adda shida ne rundunar sojin da ke wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta ta STF ta halaka yayin da jami’an ‘yan sanda uku suka rasa ransu.

Lamarin ya faru ne a wani artabu da bata garin a yankin Bwai dake karamar hukumar Mangu a jihar.

Kakakin rundunar tsaro ta Special Task Force (STF) a jihar, Manjo Ishaku Takwa ya ce, rundunar ta sami kiran neman agaji ne daga jami’an ‘yan sandan na musamman dake binciken masu laifi, a lokacin da suka je bincike ‘yan bindigar suka auka musu suka kashe ‘jami’an ‘yan sanda uku suka arce da makamansu.


No comments