Dakarun sojin Nijeriya sun kashe 'yan bindiga shida bayan ‘yan bindigar sun kashe wadansu 'yan sanda uku masu farin kaya, wadand...
Dakarun
sojin Nijeriya sun kashe 'yan bindiga
shida bayan ‘yan bindigar sun kashe wadansu 'yan sanda uku masu farin
kaya, wadanda suka je bincike a yankin karamar hukumar Mangu.
‘Yan
ta’adda shida ne rundunar sojin da ke wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta
ta STF ta halaka yayin da jami’an ‘yan sanda uku suka rasa ransu.
Lamarin
ya faru ne a wani artabu da bata garin a yankin Bwai dake karamar hukumar Mangu
a jihar.
Kakakin
rundunar tsaro ta Special Task Force (STF) a jihar, Manjo Ishaku Takwa ya ce,
rundunar ta sami kiran neman agaji ne daga jami’an ‘yan sandan na musamman dake
binciken masu laifi, a lokacin da suka je bincike ‘yan bindigar suka auka musu
suka kashe ‘jami’an ‘yan sanda uku suka arce da makamansu.
No comments