Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Ana Mugun Tafka Sata A Karkashin Gwamnatin Buhari – Minista Amaechi

  Ministan Sufurin Nijeriya, Rotimi Amaechi ya ce jami’an gwamnati mai ci na sata a karkashin mulkin shugaban kasa Muhammadu Buhari a boye s...

 


Ministan Sufurin Nijeriya, Rotimi Amaechi ya ce jami’an gwamnati mai ci na sata a karkashin mulkin shugaban kasa Muhammadu Buhari a boye sabanin yadda aka ake yi a fili lokacin gwamnatocin da suka gabata.

Amaechi ya ce sabanin yadda aka saba tafiyar da gwamnatocin da suka shude a Nijeriya, wannan gwamnatin da take ci ta APC ta yi iya bakin kokarin ta wajen dakile almubazaranci da dukiyar jama’a da kuma hukunta wadanda suka yi rub da ciki da kudaden talakawa.

Kamar yadda Rfi Hausa suka lanarto, tsohon Gwamnan Jihar Ribas ya ce a shekarun da suka gabata, za ka ga mutane sun zama Attajirai dare daya ba tare da an san su da wata sana’a ba, kuma babu wanda ya hukunta su, amma a karkashin mulkin Buhari ba a samun haka.

Amaechi ya ce cin hanci da rashawa ya zama ruwan dare a karkashin gwamnatocin Nijeriya da suka shude, ta yadda za ka ga mutane suna bushasha da dukiyar da ba a san inda suka samo ta ba a bainar jama’a, amma a karkashin wannan gwamnati idan za ka yi sata sai dai ka yi ta a boye, kuma idan an kama ka, zaka fuskanci fushin hukuma.

Wannan matsayi na ministan a hirar da ya yi da jaridar Daily Trust na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ‘yan Nijeriya ke zargin cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar wasu daga cikin jami’an gwamnatinsa na facaka da dukiyar jama’a.

Daga cikin wadanda ake zargi da irin wannan badakalar harda wasu ministoci da gwamnoni da shugabannin manyan hukumomin gwamnati.


No comments