Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Cikin Dare An Rushe Shagunan 'Yan Kasuwa A Samarun Zariya Ta Jihar Kaduna

A safiyar yau Asabar ne  21 ga watan Agustan 2021, masu kasuwanci a bakin titin Samarun Zariya, suka tashi da ganin wannan lamar...



A safiyar yau Asabar ne  21 ga watan Agustan 2021, masu kasuwanci a bakin titin Samarun Zariya, suka tashi da ganin wannan lamari na rushe musu shagunan da suke sana'a ba tare da sun kwashe komai na ciki ba.

Shi dai wannan rusau din an fara ne tun daga Makarantar Leather Research daura da Babban Gate din Jami'ar Ahmadu Bello Zariya, inda ya nufi 'North Gate' har zuwa kasuwar Samaru, inda aka rushe duk wata Kwantena a gefen titi. 

Wannan yasa wadanda abin ya shafa cikin alhini da tashin hankali, inda wasu ke ta kuka bisa hakan.

Bayanai sun tabbatar da cewa ma'aikatan dake kula da tsare-tsaren birni ta jihar Kaduna wato  KASUPDA  hade da rakiyar jami'an tsaro ne suka yi rusau din cikin daren jiya Juma'a 20 ga watan Agusta.

No comments