Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Don Allah Ku Rungumi Zaman Lafiya –Sakon Buhari Ga Al’ummar Jos

  Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya roki al'ummar Filato su rungumi zaman lafiya, tare da jaddada cewa gwamnatin na yin duk mai yiwuwa w...

 


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya roki al'ummar Filato su rungumi zaman lafiya, tare da jaddada cewa gwamnatin na yin duk mai yiwuwa wajen ganin an kawo karshen duk wani tashin hankali kamar yadda Rfi Hausa.

Shugaban ya yi kiran ne a wata sanarwa dauke da sa hannun mataimakinsa na musamman kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu, inda ya jaddada samun nasara tare da bukatar al’ummomin yankin su hada kai don yakar bata gari, yana mai cewa tashin hankali ba zai zama mafita ba.

Sanarwar ta ce duk da irin kokarin da gwamnati take yi wajen tabbatuwar zaman lafiya, bai kamata malaman addinai da sarakuna da sauran shugabannin al’umma su bari ana yada tashin hankali da tunzura jama’a ba.

Buhari ya ce akwai tarin matsalolin da kasar ke fama a yanzu kuma yana da muhimmanci 'yan Najeriya da sauran kasashe su fahimci kokarin da suke yi wajen kawar da duk wasu rigingimu a fadin kasar.

Wannan na zuwa ne yayin da Gwamnan Jihar Plateau Simon Bako Lalon ya ziyarci Yelwa Zangam inda aka kashe mutane sama da 30 a makon jiya inda ya gana da Basaraken Yankin da kuma mutanen da suka rasa Yan uwan su.

Bayan ziyarar mun tuntubi kwamishinan yada labarai Dan Manjang kuma ga jawabin da yayi mana akai, kuna iya latsa alamar sauti domin sauraren abin da yake cewa.


No comments