Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Fulanin Taraba Sun Mika Masu Garkuwa Da Mutane A Cikin Su

  Shugabannin kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah a Nijeriya sun mika wasu mutane 11 da ake zargin cewar masu garkuwa da mutane ga run...

 


Shugabannin kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah a Nijeriya sun mika wasu mutane 11 da ake zargin cewar masu garkuwa da mutane ga rundunar ‘yan Sandan Jihar Taraba.

Shugaban kungiyar Sahabi Tukur ya bayyana cewar sun yi hakan ne sakamakon alkawarin da suka yiwa Sarkin Muri Abbas Tafida na tona asirin wadanda ke aikata irin wannan laifi a cikin su.

Tukur ya ce sun kafa wani kwamiti a tsakanin su da ya kunshi bangarorin Fulanin dake Jihar da za su yi aiki da ‘yan sanda a kananan hukumomi 16 domin zakulo masu garkuwa da mutane da kuma aikata wasu laifuffuka.

Kwamishinan ‘yan Sandan Jihar Abimbola Sokoya ya yaba da matakin da kungiyar ta dauka na shawo kan matsalar tsaron da ta addabi yankin.

Sokoya ya kuma bukaci samun hadin kai tsakanin Jihohin Adamawa da Binuwe da kuma Taraba domin dakile ayyukan garkuwa da mutane da wasu laifuffukan da suka addabi jama’a, yayin da ya sha alwashin bai wa Fulanin goyan bayan samun nasara.

Wasu masu garkuwa da mutane guda 6 da suka tuba a wurin, an ba su Alkur’ani sun rantse cewar ba za su aikata laifin ba ko kuma satar shannun jama’a.

A watannin da suka gabata Sarkin Muri Abbas Tafida ya sha alwashin daukar mataki mai tsauri na kashe ‘yan’uwan mutanen da suka addabe su wajen garkuwa da mutane ko satar shanu ko kuma kashe jama’a a yankin kamar yadda Rfi Hausa ta labarto.


No comments