Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Kar Ku Dauki Makami Domin Kare Kan Ku – Minista Dingyadi

  Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da masu kiran cewar mutane su tanadi makamai domin kare kan su daga hare haren da ‘yan bindiga ke kai mus...

 


Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da masu kiran cewar mutane su tanadi makamai domin kare kan su daga hare haren da ‘yan bindiga ke kai musu ba tare da kaukautawa ba.

Ministan ‘yan Sandan kasar Muhammad Dingyadi ne ya bayyana hakan, bayan kiran da Gwamnonin Katsina da Binuwe suka yi wa jama’ar su cewar su nemi makamai domin kare kan su daga wadannan mahara.

Dingyadi ya ce saboda ‘yancin da ake da shi a Nijeriya kowa na da hurumin bayyana ra’ayinsa, amma abin sani shi ne jami’an tsaro suna iya bakin kokarin su, kuma abin da ake bukata daga jihohi shi ne samar da jami’an tsaron Anguwanni da za su taimaka musu.

Ministan ya ce sojoji da ‘yan Sandan dake aiki domin kare lafiyar jama’ar kasar na bukatar goyan bayan kowanne dan kasa na gari, yayin da ake bukatar mutane su dinga sa ido akan abin da ke faruwa a yankunan su suna kuma shaidawa jami’an tsaro domin daukar mataki kamar yadda rahoton RFI Hausa ya tabbatar.

Ganin yadda karuwar hare hare da ‘yan bindiga ke kai wa suna hallaka rayukan jama’a da kuma sace dukiyoyi ba tare da kaukautawa ba, ya sa jama’a korafi game da rawar da gwamnati ke takawa wajen kare lafiyar su.

Jihar Katsina da Zamfara da Binuwe na daga cikin wadanda ke fuskantar irin wadannan hare hare, abin da ya sa gwamnonin su fusata da kuma umurnin jama’a da su kare kan su.

Gwamnan Katsina Aminu Bello Masari ya ce gara mutane su sayi makamai maimakon biyan kudin fansa.


No comments