Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

MAAUN Ta Taya Hajiya Mairo Saidu Murnar Zama Shugabar Makarantar Aikin Jinya Ta Kano

  Shugaba kuma wanda ya kafa Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN), Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da mahukumtan jami’ar, sun t...

 


Shugaba kuma wanda ya kafa Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN), Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da mahukumtan jami’ar, sun taya Hajiya Mairo Saidu murnar nadinta a matsayin Shugabar Makarantar Aikin Jinya da Unguwanzoma ta Kano wato ‘School of Nursing and Midwifery’.

Hajiya Mairo Saidu ta kammala karatun ta a Jami'ar Maryam Abacha American University dake Jamhuriyyar kasar Nijer.

Sakon taya murnar na dauke ne a takardar da Farfesa Abubakar Gwarzo ya sanyawa hannu kuma aka rabawa ‘yan jarida a Kano a ranar Laraba.

Shugaban MAAUN  ya  bayyana nadin Hajia Mairu Saidu a matsayin shugabar makarantar da gwamnatin jihar Kano ta yi a matsayin; “nadin da ya cancanta' idan aka yi la'akari da gogewa da aiki tukuru yayin da take daliba a Jami'ar”.

Farfesa Abubakar Gwarzo ya bayyana fatansa na cewa nadin da aka yi mata za ta yi amfani da godewarta wajen gudanar da Kwalejin da zimmar ciyar da makarantar gaba.

 “a madadin kaina da iyalina da hukumar gudanar da MAAUN, ina son taya ki murna bisa nadin da aka yi miki a matsayin shugabar Kwalejin Aikin Jinya da kuma Unguwanzoma ta Kano”, inji Farfesa Gwarzo.

Ya kara da cewa; “Da fatan Allah madaukakin Sarki ya taimake ki wajen sauke sabon nauyin da aka dora miki”, inji Farfesa Gwarzo a takardar da ya rubuta.

A karshe ya yi addu’ar Allah madaukakin Sarki ya bai wa Hajia Mairo Saidu kwarin guiwa, jajircewa da hikimar shugabantar Kwalejin cikin adalci da daidaito.


No comments