Daga Hagu: Shaikh Ibraheem Zakzaky da Dan Uwansa Malam Abdulkadir Yaqoub zaune a gidansa dake Gyallesu kafin a akai ga rushewa. Daga M...
![]() |
Daga Hagu: Shaikh Ibraheem Zakzaky da Dan Uwansa Malam Abdulkadir Yaqoub zaune a gidansa dake Gyallesu kafin a akai ga rushewa. |
Daga Muhammad A. Dalhatu
- Idan Ya Zabi Ya Dawo Unguwarnan, Tabbas Muna Maraba
A
makon da ya gabata ne Babban Editan MADOGARA ya yi tattaki zuwa Unguwar
Gyallesu dake karamar hukumar Zariya ta jihar Kaduna domin jin ra’ayin mazauna
Unguwar dangane da sakin da kotu ta yi wa Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya
wanda aka fi sani da ‘yan Shi’a, Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa Zeenat
Ibrahim.
Sai
dai a tattakin da Editanmu ya yi zuwa Unguwar Gyallesu inda Shehin
Malamin ke zaune kafin a kama shi, ya tadda gidansa ya zama kufai, ba komai sai
fili cike da ciyawa. Baya ga duba muhallin, Editanmu ya gana da wadansu ba’adin
al’umma da suke zaune a Unguwar inda suka bayyana masa cewa tabbas suna mai matukar
farin cikinsu da sakin Shehin Malamin da aka yi. “gaskiya na yi matukar farin
ciki da sakinsa da kotu ta yi. Domin tabbas an zalunce sa. Kuma mutanen da suke
adawa da shi a Unguwar nan suna yi ne ba don komai ba sai saboda bambancin
akida, tabbas sun zalunce shi da karairayinsu, kuma Allah zai saka masa”, inji Abubakar
Muhammad daya daga cikin mazauna Unguwar wanda ya kai shekaru 25 yana zaune a
Unguwar.
Shi
ko Magaji Musa wani mazauni Unguwar wanda ya ce yanzu shekarunsa kusan 40 a
duniya ya bayyana mana cewa; “maganar gaskiya shi ne, Shaikh Zakzaky bai cutar
da kowa a Unguwar nan ba. Bilhasalima mutum ne da ya san hakkin makwabtansa
kuma yana saukewa. Akwai wadanda musamman a Unguwar nan wadanda ya hada da
Dattijai, Tsoffi da Malamai wadanda Shehin Malamin yake girmama su har ma yana
taimaka musu da kudi ko wani taimako idan ya taso, kowa ya sannan wannan komin
kiyayyarka da shi. Hatta kofofin da aka sanya a Gyallesu da kudinsa aka sanya
su”, ya jaddada mana.
A wani bangare na bayaninsa, wani matashi da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana mana cewa;
“duk wanda ka ga yana maganar wai ba ya son wannan mutumin (Zakzaky) ya dawo Gyallesu, wallahi dan Izala ne ko Basalafe, a don haka ba abin mamaki bane don dan Izala ko Basalafe ya tsani Zakzaky saboda ya san Zakzaky shi ne shugaban Shi’a a Nijeriya. Ni iyayena a nan Unguwar suke zaune, nima haka, kuma wallahi ina kaunar Zakzaky saboda Allah”, ya jaddada.
Kazalika,
mun samu tattaunawa da wani Dattijo wanda ya ce ba ya son a ambaci sunansa a
rahoton, amma ya bayyana mana cewa yanzu shekarunsa fiye da 50, kuma ya dade a
Unguwar a zaune, ya tabbatar mana da cewa; “tabbas a farko-farkon shekarar 2015
akwai hatsaniyar da aka samu a tsakanin wasu ‘yan iskan Unguwar da wasu da ba
su da ra’ayin Malam Ibraheem inda suka tayar da fitina wanda su kuma mabiyan
Zakzaky din suka maida martani domin kare Malaminsu, amma a ce Malam Ibraheem
ba shi da hali mai kyau na zamantakewa wannan ba gaskiya bane, amma idan kana
kiyayya da shi saboda wata manufa ta ka, to mutum zai iya fadin hakan. Amma mutum
ne (Zakzaky) mai kyautatawa hatta ga wadanda ya san a Unguwar suna cutar da shi
ne ma”, ya nusasshe.
Fatima
Khalifa (ba asalin sunanta ba ke nan), ta bayyana cewa ita ta ji dadin sakin
Shehin Malamin, domin a cewarta an zalunce shi; “kuma idan ya zabi ya dawo
Unguwarnan, tabbas muna maraba da dawowarsa. Gaskiya ni a ra’ayina zan yi matukar
farin ciki”, ta nanata.
KOTU
TA SAKI EL-ZAKZAKY
Awatan
jiya ne Babbar Kotun Jihar Kaduna a karkashin Mai Shari’a Gideon Kurada ta
bayar da umarnin a saki Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa Zeenat Ibrahim, inda
ta wanke su daga dukkan zarge-zargen da ake yi musu baki daya.
GANAWARSA
DA WADANSU BA’ADIN ALMAJIRANSA
Bayan
sakinsa da aka yi nan take tun a kotun a ranar Laraba, Shehin Malamin ya yi
ganawar farko a karshen makon da aka sake shi da wadansu ba’adin almajiransa a Birnin
Tarayya Abuja. Kuma tuni hankali ya koma
kan yadda zai dawo ya ci gaba da harkokinsa, inda ba a tantance ko a gidansa ne
da aka rushe dake Unguwar Gyallesu zai dawo ya ci gaba da zama ba ko kuma zai
sauya muhalli ne.
KISAN
KIYASHI A ZARIYA
A Disambar
shekarar 2015 ce aka kama Shehin Malamin da matarsa bayan kashe mabiyansa kusan
dubu daya da da sojojin Nijeriya suka yi bisa zarginsu da tarewa shugaban
sojoji na wancan lokaci, Tukur Burutai hanya, zargin da ‘yan shi’ar suka
karyata, inda suka ce; “dama can an tsara afka musu tare da kashe su ne da
kashe Malaminsu”.
KWAMITIN
BINCIKEN KISAN KIYASHIN
Kwamitin
binciken kisan kiyashin ‘yan shi’ar da gwamnatin Kaduna karkashin Gwamna Nasir
El-Rufai ta kafa, ya tabbatar da cewa an bizne ‘yan shi’ar 347 a ramin bai daya
a Unguwar Mando a Kaduna wadanda aka kashe a yayin da sojojin suka afka musu a
Zariya, inda kwamitin ya nemi da a hukunta sojojin dake da hannu a wannan
aika-aikar, shawarar da har yanzu gwamnatin ba ta aikata ko cewa uffan a kai
ba.
No comments