Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga Da Lalata Makamansu A Kauyukan Zamfara

  Rundunar sojin Nijeriya sun fafataki ƴan bindiga daga ginin wata makaranta da ke karamar hukumar Shinkafi a jihar Zamfara a wasu hare-hare...

 


Rundunar sojin Nijeriya sun fafataki ƴan bindiga daga ginin wata makaranta da ke karamar hukumar Shinkafi a jihar Zamfara a wasu hare-haren sama.

BBC sun ce hare-haren da suka kai da jiragen yaƙi sun yi luguden wuta a yankunan Zangon Dammaka da Jajaye maboyar wani fitaccen ɗan bindiga Kachalla Haru da yaransa.

Ɗaya daga cikin dakarun hadin-gwiwar da suka kai harin a Zamfara ya shaidawa Jaridar PRNigeria cewa sun yi nasara a dukkanin samamen da suka kai a karshen mako.

A cewar dakarun anyi nasarar kashe ƴan bindiga da dama da lalata makamansu. Sannan an lalata dazukan da suke ɓuya a Sububu. Kuma an yi nasara ba tare da shafar farar-hula ba.

Wata majiya ta tabbatarwa PRNigeria cewa an kashe sama da ƴan bindiga 50 da lalata makamansu da babura a kauyen Gidan Rijiya.

No comments