Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Su Wa Suka Kashe Alaramma Malam Ali Birnin Kudu?

Daga Wakilinmu A ranar Juma’ar da ta gabata ne 6 ga Agustan 2021, wasu tunzurarrun matasa suka auka wa Alaramma Malam Ali da duka da sar...


Daga Wakilinmu

A ranar Juma’ar da ta gabata ne 6 ga Agustan 2021, wasu tunzurarrun matasa suka auka wa Alaramma Malam Ali da duka da sara. Daga karshe suka kwara masa fetur suka banka masa wuta, nan take rai ya yi halinsa.

Lamarin ya faru ne a wani gari da ake mira Babaldu dake karamar Hukumar Birnin Kudu a jihar Jigawa.

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya gano cewa, Malam Ali ya ari Babur din abokinsa Alaramma Malam Yusuf mai Manja ya tafi gona da shi, sai mashin din ya ba shi matsala a garin na Babaldu, sai Malam Ali ya bada ajiyarsa ya hau mota ya karasa gonarsa.

Bayan Malam Ali ya dawo daga gona da sakaliyar la’asar ana ruwa. Ya zo daukar mashin dinsa kawai sai wani mutum ya yi masa ihun barawo. Nan da nan wasu fusatattun matasa suka yo kansa da duka da sara. Nan take suka kashe shi, suka banka wa gawarsa wuta. Daga bisani suka tura mashin din nasa zuwa wajen ‘yan sanda.

“Ni ba barawo bane. Ni dan Birnin Kudu ne. Ni ne Sakataren masu zazzaba shinkafa a garin Sara, ga wayata ku kira ku tambaya”, inji Marigayi Alaramma Malam Ali lokacin da suka fara dukansa. Amma duk da haka fusatattun matasan nan suka ce karya yake, suka ci gaba da dukansa har ya rasu.

“mun kama barawon babur mun kashe shi, mun kone shi kurmus, ga mashin din da ya sato, kuma ko gobe muka kara kamawa za mu kashe”, inji daya daga cikin makasan.

An gano cewa Malam Ali ne aka kashe a Babaldu a ranar Talatar da ta gabata bayan rashin dawowarsa gida tun ranar Juma’a. Sai aka samu labarin cewa wanda aka kashe din nan a Babaldu mashin dinsa yana wurin ‘yan sanda.

Mai mashin din, Alaramma Malam Yusuf mai Manja ya tafi wurin ‘yan sanda. Yana zuwa kuwa ya ce lallai wannan mashin dinsa ne. A nan take ta tabbata cewa Malam Ali ne aka kashe a Babaldu.

Da yake zantawa da manema labarai, DSP Lawal Shi’isu, wanda shi ne jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda ta jihar Jigawa, ya tabbatar da aukuwar lamarin. Ya ce; “yanzu haka mun kama mutum kusan 20, kuma suna sashen binciken manyan laifuka na CID ana bincike a kansu, kuma da zarar mun kammala bincike za mu gurfanar da su a gaban kotu don su girbe abin da suka shuka”.

Bayan samun wannan tabbaci ne, ‘yan’uwa da abokan arziki suka isa wurin da aka bizne shi a Babaldu suka tono shi suka dawo da abin da ya rage na jikinsa aka shirya shi, kamar yadda adddinin Musulunci ya tanada aka yi masa sallah a babban Masallacin Biirnin Kudu aka raka shi makwancinsa.

Wannan al’amari dai ya sosa zuciyar al’ummar wannan yanki na Birnin Kudu gaba daya, inda ya zama shi ne abin da ake tattaunawa a wannan lokaci, kuma kowa yake yi wa dan’uwansa jaje.

“Yaushe ne jama’a za su daina daukar doka a hannunsu, mutane su rika kashe mutane haka kawai babu bincike. Kowa ya zama Alkalin kansa, mutane suna zaune kamar babu hukuma?” inji daya daga cikin iyalan mamacin.

Wasu jama’a kuwa sun dora alhakin a wuyan Hukuma, domin ita ce alhakin kula da rayuka da dukiyoyin al’umma suka rataya a wuyanta.

Yanzu dai jama’ar wannan yanki na Birnin Kudu sun zuba ido su ga irin hukuncin da za a zartarwa ilahirin wadanda ake zargi da hannu wurin kisan wannan bawan Allah.

Malam Ali dai Alaramma ne, manomi, kuma dan kasuwa. An ce ya rubuta Kur’ani sau biyu da hannunsa. Ya rasu ya bar mata daya da ‘ya daya.


Kwafowa daga Jaridar Almizan ta wannan makon.

No comments