Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Sama Da 210 A Habasha

  Hukumar kare hakkin Bil Adama a kasar Habasha ta bayyana cewar 'yan bindiga sun kashe mutane sama da 210 a Yankin 'Yammacin kasar ...

 


Hukumar kare hakkin Bil Adama a kasar Habasha ta bayyana cewar 'yan bindiga sun kashe mutane sama da 210 a Yankin 'Yammacin kasar abinda ya haifar da daukar fansa kamar yadda RFI Hausa ta labarto.

Hukumar tace mazauna yankin da aka kashe mutanen ne suka shaida mata yadda Yan bindigar suka kashe wadannan fararen hula 210 a harin da aka kai ranar 18 ga watan nan, bayan janyewar jami’an tsaro daga wani sashe na yankin Oromia, daya daga cikin yankunan da ake fama da tashin hankali a cikin kasar.

Shaidun gani da ido sun ce Yan bindigar na alaka da kungiyar neman ‘yancin Oromia ta OLA, wadda ake zargi da yawan hare haren da ake samu a yammaci da kuma kudancin kasar Habasha.

Hukumar kare hakkin Bil Adamar tace kisan ya sanya mazauna yankin mata da yara yin kaura zuwa yankunan dake makotaka da su domin kaucewa harin daukar fansa a rikicin dake da nasaba da kabilanci wanda kafin wannan yayi sanadiyar kashe mutane 60.

Kungiyar OLA ta fice daga cikin OLF wadda jam’iyyar siyasa ce dake ta kwashe shekaru da dama tana gudun hijira a kasar waje kafin hawa karagar Abiy Ahmad a shekarar 2018 wanda ya bata umurnin dawowa gida.

Gwamnatin Abiy na zargin OLA da aikata kisan gilla da dama akan yan kabilar Amhara, wadda itace kabila ta biyu mafi yawa a kasar, zargin da kungiyar tayi watsi da shi.


No comments