Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

‘Yan Siyasa Ne Suke Jefa Nijeriya Cikin Matsaloli -Rochas

  Tsohon gwamnan jihar Imo Chief Rochas Okorocha ya ce 'yan siyasar Nijeriya suna taka gagarumar rawa game da barakar da ke wakana tsaka...

 


Tsohon gwamnan jihar Imo Chief Rochas Okorocha ya ce 'yan siyasar Nijeriya suna taka gagarumar rawa game da barakar da ke wakana tsakanin kabilu da mabiya addini daban-daban na kasar, lamarin dake barazana ga makomar ci gaba da hadin kan al'umar kasar.

Okorocha ya bayyana hakan ne yayin wata hira ta musamman da ya yi da Muryar Amurka.

Okorochas na magana ne kan taron daurin auren Yusuf Buhari, da ga shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari da aka yi a garin Bichi na Jihar Kano a karshen makon jiya, inda ya ce yadda manyan ‘yan siyasa suka hada kai a wurin auren ya nuna a fili cewa, 'yan siyasar na iya magance matsalolin kasar da kansu.


No comments