An sace kwamishinan yada labarai ta jihar Neja, Alhaji Muhammed Sanni Idris. MADOGARA ta labarto cewa; an sace shi ne a gidansa dake B...
An sace kwamishinan yada labarai ta
jihar Neja, Alhaji Muhammed Sanni Idris.
MADOGARA ta labarto cewa; an sace shi
ne a gidansa dake Baban Tunga a karamar
hukumar Tafa ta jihar da safiyar ranar Litinin.
Sakataren gwamnatin jihar Neja, Alhaji Ahmed Ibrahim
Matane, ya tabbatar da batun sace kwamishinan, inda ya ce an sace shi ne da
misalin karfe 1 na dare.
Sai dai ya ce jami’an tsaro sun baza
komarsu domin gano wadanda suka sace shi, inda ya bayyana kyakkwan fata na cewa
za a gano inda yake tare da karbo shi cikin aminci da koshin lafiya.
No comments