Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

An Saki Dalibai 75 A Zamfara Bayan Shafe Kwana 13 A Hannu ‘Yan Bindiga

  Daga Ammar Muhammad Bayan shafe kwanaki 13 a hannun ‘yan bindiga, daliban da aka yi garkuwa da su na makarantar Sakandaren Gwamnati dake...

 


Daga Ammar Muhammad


Bayan shafe kwanaki 13 a hannun ‘yan bindiga, daliban da aka yi garkuwa da su na makarantar Sakandaren Gwamnati dake Kaya a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara sun shaki iskar ‘yanci.

Gidan Talabijin na kasa, NTA ne ya wallafa labarin a sahihin shafinsa na Facebook a ranar Litinin.

NTA ta labarta cewa dalibai guda 75 sun samu ‘yancinsu, amma ba su yi karin bayani kan yadda aka ‘yanto daliban ba.

Labarin na NTA ya wallafa cewa ne; “Dalibai 75 na makarantar Sakandaren Gwamnati dake Kaya a karamar Hukumar Maradun ta jihar Zamfara, wadanda aka yi garkuwa da su mako biyu da ya gabata, sun shaki iskar ‘yanci”.

A ranar 1 ga watan Satumban 2021 ne, ‘yan sandan jihar Zamfara, suka bayyana labarin sace daliban bayan da ‘yan bindiga suka kai wa makarantar hari.


No comments