Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

An Yi Watsi Da Ayyuka Fiye Da Dubu 13 A Yankin Neja Delta - Rahoto

  Ministan kula da Harkokin Neja Delta, Sanata Godswill Akpabio ya ce rahoton binciken da aka yi kan Hukumar Ci gaban yankin na Neja Delta N...

 


Ministan kula da Harkokin Neja Delta, Sanata Godswill Akpabio ya ce rahoton binciken da aka yi kan Hukumar Ci gaban yankin na Neja Delta NDDC, ya nuna cewa akwai ayyuka sama da dubu 13 da aka yi watsi da su a yankin.

Sanata Akpabio ya bayyana hakan ne a  ranar Alhamis a Abuja, lokacin da ya mika rahoton binciken ga shugaban kasa Muhammadu Buhari ta hannun ministan shari’a, Abubakar Malami.

Akpabio ya ce tun kafin gabatar da rahoton wasu ‘yan kwangila suka koma kan aikin su da kan su, kuma kawo yanzu sun kammala ayyukan hanyoyi kusan 77.

Yankin na Neja Delta na ci gaba da zama koma baya tun daga shekarar 1958, duk da kokarin gwamnatocin baya ta hanyar kirkirar shirye -shirye da ayyuka daban-daban domin bunkasa yankin.

A halin da ake ciki dai, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta tabbatar ta kwato sama da Naira tiriliyan 6 da ake zargin an karkatar da su a yayin gudanar da ayyukan hukumar NDDC tsakanin shekarar 2001 zuwa 2019.


No comments