Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Ana Ci Gaba Da Neman Dalibin Da Hotonsa Ya Yadu A Intanet A Keke Domin Tallafa Masa

  Hoton wani dalibi dan Nijeriya a kan Keke a daidai lokacin da ake ruwan sama ya ja hankalin ma’abota shafukan sada zumunta musamman a Face...

 


Hoton wani dalibi dan Nijeriya a kan Keke a daidai lokacin da ake ruwan sama ya ja hankalin ma’abota shafukan sada zumunta musamman a Facebook, inda aka baza cigiyar nemansa domin gano inda yake don a ba shi tallafi na musamman.

Dalibin wanda hoton ya nuna shi sanye da kayan makaranta farare a kan Keke yana zuba gudu akan Kekensa domin isa makaranta, ya ja hankalin wani dan Nijeriya ma’abocin shafukan sada zumunta mai suna Ibrahim Sanyi-Sanyi, inda ya baza hoton na shi yana neman inda za a gan shi.


Hoton Dalibin

Ibrahim Sanyi-Sanyi ya wallafa hoton dalibin a turakarsa ta Facebook, inda ya nemi jama’a da su taimaka masa wajen gano inda dalibin yake, inda ya ce suna son bai wa wannan dalibi mai kwazo gudummawa ne.

Mutane da dama suma sun alkawuranta cewa za su tallafa wa dalibin in dai har an gano shi wajen ganin dalibin ya cimma gaci.

Ya zuwa hada rahoton nan, cigiyar dalibin, mutum 630 ne suka raba shi ga sauran abokansu a Facebook din.


No comments