Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja a yau Lahadi zuwa New York domin halartar Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA76) na...
Shugaban
kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja a yau Lahadi zuwa New York domin halartar
Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA76) na 76.
Zaman
zai fara ne daga ranar Talata, 14 ga watan Satumba.
Taken
taron na UNGA na wannan shekara shi ne: "Gina Tsarin Rayuwa mai cike da
Fata-Don Warkewa daga COVID-19, Sake Ginawa Mai Dorewa, Amsa Buƙatun Duniya,
Girmama Haƙƙin Mutane da Rayar da Majalisar Dinkin Duniya."
Shugaban
na Nijeriya zai yi jawabi ga Majalisar a ranar Juma'a, 24 ga watan Satumba inda
zai yi jawabi kan jigon taron da sauran batutuwan da suka shafi duniya.
Femi
Adesina, mai magana da yawun shugaban, shi ne ya tabbatar da hakan a cikin wata
sanarwa da ya fitar a ranar Asabar inda ya ce Shugaba Buhari da mrmbobin
tawagarsa za su kasance cikin wasu muhimman tarurruka.
No comments