Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Cutar Kwalara Ta Kashe Mutum Fiye Da 150 A Katsina

  Gwamnatin jihar Katsina ta ce zuwa yanzu mutane sama da 150 aka tabbatar mutuwarsu daga cikin wasu akalla dubu 5 da 677 da suka kamu da cu...

 


Gwamnatin jihar Katsina ta ce zuwa yanzu mutane sama da 150 aka tabbatar mutuwarsu daga cikin wasu akalla dubu 5 da 677 da suka kamu da cutar Kwalara, tun bayan barkewar a jihar kimanin wata guda da ya gabata.

Babban Sakataren Hukumar Kula da Kula da Lafiya a matakin Farko a Katsina, Dakta Shamsudeen Yahaya, ya shaidawa manema labarai cewa, an tattara alkaluman ne daga asibitoci da sauran cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko da ke jihar.

Jami’in ya kuma bayyana fargabar adadin wadanda suka mutu na iya zarta wanda aka kididdige, kasancewar akwai mutane da dama musamman a karkara, da ba sa zuwa asibiti.

A farkon watan Agusta hukumomin jihohin Sokoto da Zamfara suka sanar da mutuwar mutanen da yawansu ya kai 53, 30 daga cikin su Zamfara, yayin da 23 suka mutu a Sokoto.

No comments