Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Dattawan Jihar Filato Na Bukatar Bincike Akan Tura Wasu Matasa Isra'ila Da Jang Ya Yi

  Rfi Hausa ta labarto cewa; ana ci gaba diga ayar tambaya tun bayan gudanar da babban taron manema labarai a makon jiya wanda Kwamitin Da...

 



Rfi Hausa ta labarto cewa; ana ci gaba diga ayar tambaya tun bayan gudanar da babban taron manema labarai a makon jiya wanda Kwamitin Dattawan Jam’iyyar APC, reshen jihar Filato ta Najeriya ya shirya don bita kan sha'anin tsaro, inda ake neman bayani akan wasu matasa 300 da tsohuwar gwamnatin jihar ta tura Isra'ila domin samun horo.

A yayin gudanar da taron a ranar 3 ga watan Satumba, kwamitin ya bukaci Gwamnan jihar Simon Lalong da ya sake nazartar badalakar daukar wasu matasa aikin tsarom da tsohon Gwamnan jihar Jonah Jang ya yi tare da tura su Isra’ila domin samun horo.

A zamanin mulkinsa, an ruwaito cewa, Jang ya dibi matasa 300 tare da tura su Isra’ila don ba su horo kan tsaro, amma tun bayan dawowarsu, har yanzu ba a ji duriyarsu ba.

Bayanai sun ce, akasarin matasan ‘yan kabilar Birom ne, wato kabilar tsohon Gwamnan, kuma an yi zargin cewa, ya dibe su ne domin cimma wata manufa ta murkushe abokan gaba a jihar amma ba don masalahar al'umma ba.

Jang ya mulki jihar Filato a tsakanin shekara ta 2007 zuwa 2015, yayin da a zamaninsa aka samu asarar dubban rayukan jama’a da kuma salwantar kadarori na biliyoyi a rikice-rikicen kabilanci.

Tsohuwar gwamnatin Jang ta PDP ta hakikance cewa, domin tabbatar da tsaro a jihar ta samar da rundunar matsan a wancan lokaci.

Yanzu haka kwamitin dattawan APC ya bukaci Gwamna mai ci da ya lalubo wadannan matasa domin amfani da su wajen samar da tsaro a jihar, lamarin da ya zafafa muhawara kan lamarin.

Wannan muharawa dai, ta tayar da sabuwar kura a jihar ta Filato wadda ke cika shekaru 20 da fara mummanar tashin hankalin da ya haifar da rasa dimbin rayuka ranar 7 ga watan Satumabr shekarar 2001 a karkashin mulkin tsohon Gwamna Joshua Cibi Dariye.

An dai gudanar da taron manema labaran ne ganin yadda lamurran tsaro suka kara sukurkucewa a  baya-bayan nan jihar ta Fliato.


No comments