Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Gwaggo Na Landan A Yayin Da EFCC Ke Nemanta Bayan Dan Gwaggo Ya Kai Kararta

  Gwamna Dr Ganduje a Hagu tare da matarsa, Farfesa Hafsat Ganduje Daga Auwal Adam A daidai lokacin da Babban Dan Gwamna Dr Abdullahi Umar...

 

Gwamna Dr Ganduje a Hagu tare da matarsa, Farfesa Hafsat Ganduje


Daga Auwal Adam

A daidai lokacin da Babban Dan Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje,wato Abdul’aziz Ganduje ya kai karar mahaifiyarsa Farfesa Hafsat Ganduje gaban Hukumar yaki da rashawa, EFCC kan zargin da yake yi mata da almundahana da kuma azurta kanta ta hanyoyin da yake ganin ba su dace ba, a yau Talata, AbubakarAminu Ibrahim, mai tallafawa Gwamnan Abdullahi Ganduje kan kafofin sadarwa na zamani ya wallafa hotunan Gwamna Abdullahi Umar Ganduje  OFR, da Uwargidansa Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje da sauran iyalansa a lokacin da suka halarci bikin yayen Dalibai wanda ya hada da Dan Autansu Muhammad Abdullahi Umar wanda ya kammala Jami'ar ‘Regent’s University’ dake Landan inda ya yi digirinsa na farko a bangaren 'Global Management (Enterprise & Innovation)'.


Muhammad Abdullahi Umar (daga dama sanya da rigar yayen dalibai) tare da iyayensa da sauran iyalai. 

An yi bikin ne a yau Talata 14 ga watan Satumban 2021. Abubakar Aminu bai yi karin bayani kan bikin yayen daliban ba, sai dai hotuna da ya wallafa har kashi biyu dangane da bikin yayen daliban.

Rahotanni sun bayyana cewa; Babban dan Gwamnan jihar Kano, Abdul'aziz Ganduje ya maka mahaifiyarsa Dr Hafsat Ganduje a gaban hukumar yaki da yi wa tattalin arziki zagon kasa wato EFCC akan zargin da yake yi mata da almundahana da kuma azurta kanta ta hanyoyin da yake ganin ba su dace ba.

Tuni dai a bangaren Hukumar EFCC din ta aikewa da Dr Hafsat Ganduje mai dakin Gwamnan Kano da goron gayyata domin ta je gaban Hukumar don amsa tambayoyi kan zargin da dan na ta ke yi mata, amma ta ki amsa gayyatar ba tare da kuma ta bayar da wani uzuri a rubuce ba.

A cikin wasikar da Abdul'aziz Ganduje ya aikewa da EFCC, ta shafi badakalar filaye da kuma miliyoyin kudade. Sai dai Kakakin Hukumar EFCC Wilson Uwujaren bai ce uffan ba dangane da batun bayan an yi masa tambaya a kai.

Idan ba a manta ba, a baya an zargi Gwamnan Kano Alhaji Abdullahi Umar Ganduje da yin badakala ta sama da dalar Amurka miliyan biyar, inda aka nuno shi a wani faifan bidiyo yana sunkuma dalar Amurka daga cikin kudaden 'yan kwangila, sai dai Gwamnan ya karyata bidiyon tare da kai karar jaridar Daily Nigerian da mawallafinta Jaafar Jaafar gaban kotu game da batun bidiyon Dala.


Muhammad Abdullahi Umar, Dan Autan Ganduje da ya kammala digirinsa na farko



No comments