Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Harin DSS A Gidan Igboho: Gwamnatin Tarayya Ta Daukaka Kara Kan Hukuncin Babbar Kotu -Malami

  Gwamnatin Tarayya ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin babbar kotun jihar Oyo wacce ta ce a bayar da diyyar Naira Biliyan 20 kan Babban L...

 


Gwamnatin Tarayya ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin babbar kotun jihar Oyo wacce ta ce a bayar da diyyar Naira Biliyan 20 kan Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF) da Hukumar Tsaro ta DSS saboda zargin mamaye gidan Sunday Adeyemo da Hukumar DSS ta yi a ranar 1 ga watan Yuli.

Kotun da ke zama a Ibadan ta bayar da wannan umurnin bayar da wannan diyyar ne a cikin karar kare hakkin dan adam wanda mai fafutukar kafa kasar Yarbawa, Adeyemo, wanda aka fi sani da Igboho, ya kai a kan wadanda yake tuhumar saboda mamaye gidansa da ke yankin Soka a babban birnin jihar Oyo.

AGF, Mista Abubakar Malami (SAN), duk da haka, ya shaida cewa a ranar Juma’a Gwamnatin Tarayya za ta daukaka kara kan hukuncin, kuma tuni aka fara shirin daukaka karar.

Lauyan Igboho, Mista Yomi Aliyu (SAN), shi ne wanda ya shigar da kara na neman hakkin bil adama da yake ganin an take wa wanda yake bai wa kariya, inda ya nemi AGF, DSS da Daraktan DSS na Oyo su biya Naira Biliyan 500.


No comments