Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Jami’ar Maryam Abacha Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Dalibinta Muhammad Aisami

  Hukumar gudanarwa ta Jami’ar Maryam Abacha American University dake Nijer, ta mika sakon ta’aziyyarta ga Iyaye da ‘yan’uwan daya daga ciki...

 


Hukumar gudanarwa ta Jami’ar Maryam Abacha American University dake Nijer, ta mika sakon ta’aziyyarta ga Iyaye da ‘yan’uwan daya daga cikin dalibanta, Muhammad Ahmad Aisami, wanda ya rasu sakamakon hadarin mota a titin Gubio zuwa Maiduguri a ranar Litinin din 13 ga watan Agustan 2021.

Marigayi Muhammad Aisami yana matakin aji biyu ne (200 level) A Jami’ar a sashen gudanar da al’umma (Public Administration).

Sakon ta’aziyyar na dauke ne da sa hannun shugaba kuma mu’assasin Jami’ar Maryam Abacha American University da Franco-British International University dake Kaduna, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, wanda aka raba wa manema labarai kwafinta a Kano a ranar Talata.

Hukumar gudanarwa ta Jami’ar ta bayyana rasuwar dalibin a matsayin babban rashi ba kawai ga Iyayensa da ‘yan’uwansa ba, ga dukkanin ma’aikatan makarantar.

Shugaban MAAUN har wala yau ya bayyana Marigayin a matsayin dalibi mai ladabi wanda ke girmama Dattawa, musamman Malamansa.

Farfesa Abubakar Gwarzo ya ce "A madadin Hukumar Gudanarwar ta Jami'ar Maryam Abacha American University ta Nijer, ina mika sakon ta'aziyya ga iyaye, 'yan uwa da abokan Muhammad Ahmad Aisami bisa rasuwarsa." Inji Farfesa Abubakar Gwarzo.

Ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya sanya Marigayin a Aljannah Firdaus ya kuma bai wa iyalansa jure wannan rashin da ba za a iya maida shi ba.


No comments