Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Jirgin Yaki Ya Kashe Fararen Hula A Jihar Yobe

  Wani jirgin yaki ba a tantance daga ina yake ba ya yi aman wuta a yankin kauyen Buhari da ke karamar Yunusari a jihar Yobe da safiyar La...

 



Wani jirgin yaki ba a tantance daga ina yake ba ya yi aman wuta a yankin kauyen Buhari da ke karamar Yunusari a jihar Yobe da safiyar Laraba, inda ya yi sanadin mutuwar fararen hula da dama.

Al'ummar garin sun ce shaida wa BBC cewa sun wayi gari ne da ganin jiragen yaki har uku suna shawagi a sararin samaniyar garin nasu.

Daga bisani daya daga cikin jiragen ya yi aman wuta kan wani bangaren garin, kamar yadda wani da 'yan uwansa suka mutu a lamarin ya shaida wa BBC.

BBC ta tuntubi runudnar 'yan sandan jihar Yobe inda Kakakinta ASP Dungus Abdurrahman ya ce ba su samu labarin ba, amma za su tuntubi BBC idan suka samu labarin.

"Da safe kamar karfe 8.30 ne abin ya faru, har zuwa lokacin da daya daga cikin jiragen ya fado wani bangaren na garin yana ta zubar da wuta, duk gidajen da ke wannan bangaren sai da suka lalace.

"Jirgin babba ne sosai irin na sojoji, amma ba mu san na ina ne ba," in ji shi.

Ganau din ya ce ba za su iya sanin adadin mutanen da suka rasu ba zuwa yanzu, "don ko a cikin gidanmu ma mun rasa mutum biyu," in ji shi.

Ya ce cikin mamatan gidansu akwai matar babansa da 'yar yayarsa, "amma ni ba na gida lokacin muna gefen gari a kan idonmu komai ya faru.

Sai dai ya ce har yanzu babu jami'in tsaron da ya je wajen, "don da akwai yaran Boko Haram da ke shawagi sosai a yankin."

Ganau din ya ce su 'yan gari ya su-ya su ne suka yi aikin kwasar gawarwaki da wadanda suka jikkata zuwa asibitin garin Geidam, saboda rashin kyawun sadarwa ma ba zai sa su tsaya bata lokacin yin waya ba, kamar yadda ya ce.

Shi ma wani mazaunin garin da aka je asibitin Geidam da shi ya cewa BBC halin da wadanda suka jikkatan ke ciki ba shi da dadin gani sam.

"Idan ka kalle su ba za ka iya sake kallonsu ba don duk suna cikin jini kaca-kaca babu dadin gani.

"Da idona na ga mutum 19 da suka jikkata. Akwai wadanda suka rasu da dama kuma amma ba a san adadinsu ba don an bar su a can garin Buharin.

"Ni ma akwai dangina hudu da suka jikkata," ya ce.

Amma mutumin ya ce a can Geidam akwai jami'an tsaro da dama da suka zagaye asibitin.

-BBC Hausa


No comments