Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Kungiyar NLC Ta Gudanar Da Addu'ar Samun Nasara Kan ‘Yan Bindiga A Zamfara

Daga Hussaini Ibrahim, Gusau Kungiyar Kwadago ta kasa reshen jihar Zamfara, ta gudanar da taron addu'a domin samun nasara akan yakin...


Daga Hussaini Ibrahim, Gusau

Kungiyar Kwadago ta kasa reshen jihar Zamfara, ta gudanar da taron addu'a domin samun nasara akan yakin da Gwamnati ke yi da ‘yan Bindiga da suka addabi al'ummar Jihar Zamfara.

Shugaban Kungiyar na Jihar Zamfara, Kwamared  Sani Halliru ne ya jagoranci gabatar da addu'ar a hedikwatar kungiyar da ke Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

Kwamared Sani Halliru ya bayyana cewa, ‘yan Bindigar sun gurgunta ayyuka a ma'aikatun jihar ta Zamfara sakamakon dauki dai dai da suke yi wa ma'aikatan domin neman kudin fansa, inji Kwamared Sani Halliru.

Kuma ya kara da cewa, yanzu haka a cikin satin nan ‘yan Bindigan sun yi awon gaba da Shugaban Ma"aikatan gwamnati, Kwamared Sidi Ibrahim a gidansa da ke Karamar hukumar Bukkuyum bayan sun sako Daraktan lafiya da wasu Ma'aikatan da aka biya kudin fansa; “akan haka muka shirya wannan addu'ar na ganin kudirin gwamna Matawalle da jami'an tsaro ya cika na ganin an gama da 'yan Bindiga da suka addabi Jihar Zamfara”, inji shi.

A nasa jawabin Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau, Alhaji Ibrahim Bello ya bayyana cewa, rashin taimakon 'yan’uwa ga masu hali ne da rashin zumunci ya kara jawo yin garkuwa da mutane; “domin za ka ga a gida Allah ya yi wa karami arziki bai iya taimakon Yayan sai ya bar shi ya kwana da yunwa, wannan ya sanya wasu shiga cikin gungun miyagu. Sada zumunci kuwa a nan ne mutum zai ga wanda zai taimaka a cikin danginsu idan ya ziyarce su ya ga halin da suke ciki”, inji Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau.

Kuma ya yi kira da babbar murya akan taimakon mabukata da sada zumunci, da kuma yin addu'a da sadaka domin sune ke kare masifa a cewarsa.

A nasa jawabin Shugaban Ma'aikatan Jihar Zamfara, da ya samu wakilcin Babban Sakataren a ofishinsa, Alhaji Yusuf Bakura , ya nuna jindadinsa ganin yadda kungiyar Kwadago ta damu da halin da al'umma ke ciki har ta shirya addu'a domin samun nasara akan ‘yan Bindiga da suka addabe mu.

No comments