Wakilin shugaba Biden a Koriya ta Arewa ya ce kofa a bude ta ke domin tattaunawa, kwana guda bayan kasar ta yi nasarar gwajin makami mai...
Wakilin shugaba Biden a Koriya ta
Arewa ya ce kofa a bude ta ke domin tattaunawa, kwana guda bayan kasar ta yi
nasarar gwajin makami mai linzami mai cin dogon zango.
Sung Kim na magana ne a wani taro da
aka yi a birnin Tokyo na Japan, tare da manyan jami'an gwamnatin Japan da kuma
Koriya ta Kudu.
Mista Kim ya ce ya na son bayyanawa
karara cewa Amurka ba ta da niyyar tsaurarawa Koriya ta Arewa.
Wakilai uku na tattaunawa kan hanyar
da za su karfafawa Pyongyang gwiwar komawa teburin sulhu, ana kuma sa ran za su
yi wa Arewar tayin kayan agaji a daidai lokacin da ta ke fama da matsin
tattalin arziki da karancin abinci.
-BBC Hausa
No comments