Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

MAAUN Ta Sauke Tutocinta Kasa-kasa Na Tsawon Kwana 10 Kan Rasuwar Dalibinta Muhseen Bala

Hukumar gudanarwa ta Jami’ar Maryam Abacha American University dake Jamhuriyyar kasar Nijer, ta sauke tutocinta kasa-kasa domin makokin ra...


Hukumar gudanarwa ta Jami’ar Maryam Abacha American University dake Jamhuriyyar kasar Nijer, ta sauke tutocinta kasa-kasa domin makokin rasuwar  Muhseen Bala muhammad Tukur wanda Allah ya yi wa rasuwa sakamakon rashin lafiya a ranar Alhamis din 16 ga watan Satumban 2021a Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano.

Marigayi Muhseen Bala Muhammad daya ne daga cikin daliban Jami’ar ta MAAUN  wanda ke karatun ilimin sanin kwamfuta da fasahar bayanai (Computer Information Technology) a matakin aji biyu (200 level).


Marigayi Muhseen Bala


Sakon ta’aziyyar na dauke ne da sa hannun shugaba kuma Mu’assasin Jami’ar Maryam Abacha American University da Franco-British International University dake Kaduna, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, wanda aka raba wa manema labarai kwafinta a Kano a  yau Juma’a 17 ga watan Satumban 2021.

Hukumar gudanarwa ta Jami’ar ta bayyana rasuwar dalibin a matsayin babban rashi ba kawai ga iyayensa da ‘yan’uwansa ba, ga kafatanin ma’aikatan makarantar.

Shugaban MAAUN har wala yau ya bayyana Marigayin a matsayin dalibi mai ladabi wanda yake girmama Dattawa, musamman Malamansa.

Farfesa Abubakar Gwarzo ya ce "A madadin Hukumar Gudanarwar ta Jami'ar Maryam Abacha American University ta Nijer, ina mika sakon ta'aziyya ga iyaye, 'yan’uwa da abokan musamman mahaifinsa wanda shi ne Daraktan kulla Alaka na Jami’ar, Dr Bala Muhammad Tukur da mahaifiyarsa bisa rasuwarsa",  Inji Farfesa Abubakar Gwarzo.

A karshe ya yi addu’ar Allah madaukakin Sarki ya sanya Marigayin a Aljannah Firdaus ya kuma bai wa iyalansa jure wannan rashi mai radadi.

No comments