Uwargidan Shugaban kasa, Hajiya Aisha Buhari ta wallafa wani faifan bidiyo na Ministan Sadarwa Isa Ali Pantami yana shessheka kuka a wan...
Uwargidan Shugaban kasa, Hajiya
Aisha Buhari ta wallafa wani faifan bidiyo na Ministan Sadarwa Isa Ali Pantami
yana shessheka kuka a wani darasi da yake gabatarwa a Masallacin Annur dake
Abuja, inda ta rubuta cewa; 'A cire tsoro a yi abin da ya dace'.
Aisha Buhari ta wallafa wannan sako ne a shafinta na
Instagram.
Manazarta na kalla hakan a matsayin
maida martani ga Ministan Sadarwar da Tattalin Arzikin Nijeriya dangane da
matsalar tsaron da ake fama da ita a Nijeriya duba da yadda ministan ya shahara
da yin kuka da caccakar gwamnati a gwamnatocin baya da ba a dama da shi ba a
daidai irin wannan lokaci da matsalar tsaro ya ta’azzara.
No comments