Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

MDD Ta Yi Tir Da Juyin Mulki A Guinea

  Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi Allah wadai da amfani da karfin da sojoji suka yi a Guinea wajen kwace ...

 


Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi Allah wadai da amfani da karfin da sojoji suka yi a Guinea wajen kwace mulki, inda ya bukace su da su gaggauta sakin shugaban kasar Alpha Conde.

Sanarwar da Guterres ya gabatar ta ce yana sanya ido akan abin da ke faruwa a Guinea sau da kafa, a yayin da ya bayyana takaicin #sa na amfani da karfin bindiga wajen kwace iko.

Yanzu haka al'umaran yau da kullum sun tsaya cik a birnin Conakry, inda aka rufe kasuwanni da manyan shaguna, bayan sanarwar sojojin kasar wadanda suka yi ikirarin juyin mulki tare da kama shugaba kasa Alpha Conde, duk da cewa a bangare guda gwamnati ta ce ta murkushe yunkurin ne.

Hafsan sojin da ya bayyana a kafar talabijin din kasar ya kuma sanar da rufe iyakokin sama da kasa da kuma rusa gwamnatin kasar.

 

No comments